HUBBUL YAKIN 3

  

ASIYA SADIQ MACCIDO

(ASIKHAN)



Copyright © Asiya Sadiq 7th March, 2019 to 4th March, 2020

Hakkin Mallaka (M) Asiya Sadiq 7th March, 2019 to 4th March, 2020



Published in Nigeria by

Sharhamak Computer Ventures

Beside Birnin Kebbi Local Government Secretariat

Kebbi State, Nigeria

Website: www.hausanovels.xyz



Tel: 08113777717




Hotonta ne akan screen din wayar sa`adda shekarunta ba xasu wuce 16 to 17 years ba,kamar wacca aka xarewa laka a jiki ta fara juyowa a hankali browsing din muryarda keyi mata bala`in takeyi a kwakwalwarta ,wa xata gani a gaban nata,USMAN! Ne  tsaye a cikin qananan  kaya  tamkar  wani bature,ga  baki daya numfashinta  qoqarin ficewa yakeyi daga jikinta kallonshi kawai takeyi idanuwanta a xaxxare kamar wacce  taga  axara`ilu.A fusace ya kalleta amma cin karo da yayi da fuskarta ya sanyashi kidimewa  gami da rikicewa a nan take,ga baki daya rasa ta cewa yayi kallonta kawai yakeyi wani farin ciki da jin dadi ke xiyartar  xuciyarshi sam! Ma ya rasa wace duniya yake a ciki,mema xaiyi,me xaice duk ya rasa,farin cikinda ya tsinci kanshi kuwa a ciki kai daka ganshi xaka xata anyi masa bushara ne da gidan al,janna. Qaf! taji yawun bakinta sun qafe ,ga baki dayama ta rasa me xata ce kamar kurma haka ta koma ta nemi Magana sama da qasa ta rasa,wai shin mafarkine ko gaske,usman dinne take gani a tsaye a gabanta .Kallon-kallo kawai sukeyi  sai kace wasu xakuna,kowa ya rasa me xaice.Su Hajiya Larai kuwa suka dawo baya da hanxari a sakamakon ganin abinda ke gudana da  sukayi,please kayi haquri malam bada gan-gan bane kuskurene kowa kuwa xai iya yi,Hajiya Lara ice ke bawa Usman haquri.Ga baki daya baiji ma abinda take fad aba,kafe Bilkisu kawai yayi da ido yana wani tattausan murmushi wanda yake nuna tsagworon farin ciki gami da tsantsar  so da qauna,har a ranshi so yakeyi ya janyota a jikinshi ya rungumeta,tunanuka kala-kala ne ke xuwa mishi a xuciya.Ita kuwa Bilkisu a tata xuciyar farin ciki da murna takeyi  domin kuwa gani takeyi tamkar a yau dinnan ne xata ceto mijinta wato Sulaiman,wani bangare kuwa xuciyar tata saqa mata takeyi ta dallawa Usman din mari akan irin bala’o ukan da ya jefata,Bata taba jin haushi gamida baqin cikin mutum ba sai a ranar a kuma lokacin,ba kuma ta tuna da irin tambonda Usman din yayiwa rayuwarta ba sai a yanxu da yake tsaye a gabanta.Wasu xaafafan hawae ne suka kwaranya daga idanuwanta suka dinga kwaranya akan kyakkyawar fuskarta,muryarta na rawa gami da karkarwa take fadin “NEMANKA XAMUJE”wannan Kalmar kadai ta samu ta fito daga bakinta.No! No! don’t cry Usman ne ke fadan haka fuskanshi duk a yamutse,ba sai kinje nemana b,gani na dawo a gareki Kaman yanda nayi miki al’qawari a baya cewan xan dawo a gareki,ni kadai ne mijinki a duniya,banci amanarki ba Billy koda kuwa da one second ne,kullum kina a cikin xuciya ta idan bake ba wama kike ganin xanso,kin rigani ne domin kuwa da a gobe ne nayi niyar xuwa nemanki nayi niyar xuwa neman ixnin aurenki a wurin mahaifinki domin kuwa na riga da n agama tanadar mana gamida shirya mana rayuwa mai dadi kuma mai dorewa ta har abada ni nakine  ni kadai a duniya domin  ni akayiki domin ki kasance dani ki xamo uwar yaya na,lokacinda yakai nan a xancensa qoqari yayi ya janyota ya rungumeta.amma kallonda tayi masa ya dakatar dashi daga aikata hakan.Batasan ma ta inda xata fara yi masa bayani ba,tamkar wani mara hankali take kallonshi,lallaima usman dinnan bayada hankali ta dauka shi shahararre ne a fagen iya soyayyya ashe bah aka bane,domin da kuwa ace yasan meye soyayya,kallo daya xaiyi mata ya isa ya hango a cikin idanuwanta sam ba soyayyyarshi koda kwatan kwacin kwayar xarra a ciki,da ace shi gwani ne ai da ya gano kukanda takeyi bana murnar ganinshi a matsayin masoyi wanda nake murna da farin cikin gani bane a’aina murnar  ganinshi ne a matsayinshi na makulli wanda yakeda qarfinda xai iya  bude mani qofarda xata da xata sadani da mijina,mahaifin cikinda yake a jikina yanxu haka.Hajiya Larai da Tukur ne a tsaye sun kafe su da idanu,mamaki da al’ajabi ya  hanasu Magana,sam basa buqatar a gayamusu wannan saurayin waye domin kuwa abinda idanuwansu suka gane musu kadai ya isa yasa su fahimci ko shi wanene koshi waye.Ba qaramin farin ciki sukayi ba Allah ya sauqaqe musu wahala ya hadasu dashi ba tareda sun wahala ba,su dai shiru sukayi abinsu  suka mayarda Usman din da Bilkisun t,vn su abin kallonsu,toh! Mema suka san xasu ce ne idan ba kallo kawai ba,Dogon numfashi Bilkisun tayi we need to talk Usman,mu tafi gida xamuyi Magana,yamutsa fuska yayi kana yayi murmushi okay! Mu tafi,itace ta shiga gaba Usman din ya biyota  baya kana su Hajiya Larai.Ga motar a can ta nuna masa motarsu data kawosu  a airport din,sai a lokacinne ya kula dasu Hajiya Laranda ke biyansu,tsayawa yayi cikin farin ciki yake maganar,su waye wayyan Billy,kar dais u umman ki ne kinga wallahi sam ban gansu bad an Allah kiyi haquri ban gaidasu bahankalina ne ya dauke,ganinki da nayi a kusa dani ya sanyaidanuwana rufewa da ganin kowa kafin tayi Magana tuni ya dawo baya da qarfi gaishesu yayi cikin girmamawa tareda basu haqurin rashin aikata hakan da yayi tun a farko tareda gayamusu shi sam bai gansu a wurin bane,sun kuwa amsa mishi suma sosai .Alfarma ya nema kai tsaye a wurinsu da su amince shida Bilkisu dasu amince shida Bilkisu su shiga motarda taxo daukanshi,ya nuna musu motarda take gefen damansu ya gayamusu sai su bisu a baya su isa a gidan,rasa me xasuce sukayi,kallon-kallo kawai sukeyi a tsakaninsucan hajiyar  ta samu tace ba damuwa juyowa yayi ya kalli Bilkisu wani dadi yaji a xuciyarsa kamar wanda aka bawa daman ya dauketa kawai su wuce abinsu.Kallonshi kawai tayi wani haushi da takaici duka suka cikata tama rasa me xata ce masa,Su Hajiya Larai ne suka fara bude motarsu suka shiga,sai Usman da Bilkisu kuma da suka nufi gun tasu dalleliyar mota,sabuwa gar! Da ita,da hanxari driver yaxo ya karbi kayanda ke hannun Usman  din ya nufi boot din motar da nufin ya bude boot din ya saka kayan a ciki.Usman ne yayi hanxari ya budewa Bilkisu murfin motar tareda yi mata nuni akan ta shiga.Bata kalleshi ba a wannan karon kai tsaye shiga kawai tayi,ya maida murfin ya rufe yayi sauri ya nufi nashi bangaren ya bude ya shiga,tada mota drivern yayi,motarda take gabanmu xaka bi duk inda tayi a can xakayi a can xaka kaimu,to ranka shi dade drivern ya fada tareda jan motar.Matsowa Usman din yayia kusa da Bilkisu amma a hankali taja da baya ba tareda ta kalleshi ba kota nuna qoqarinda yakeyi nan a matsowa daf da ita,kallonta yayi yayi murmushi domin kuwa ya lura da matsawarda tayi gamida shan jinin jikinta da tayi.Billy I miss you,I miss you,I miss you so much,I miss u moredan you can imagine moredan you can think up,hannunta ya janyo ya riqe yaci gaba da rero mata bayanai  da kalamai wayanda ba matar aurenda ya kamata tajisu a bakin wani idan dai ba mijinta na sunnah ba .Da hanxari ta fara yunqurin kwatar  hannunta daga gareshi amma sam! Ta kasa kwace hannun nata,dariya ya saki kana ya sake mata hannu you are still the same Billy,ya girgixa kai very soon xan kama wannan hannun naki batareda kinyi yunqurin kwacewa ba,very soon xan mallakeki da duk wani abu naki Billy,very soon xaki xama mallakina xan kuwa yi amfani da wannan hannun nawa na riqe wannan dan qaramin hannun naki always.Juyowa kawai tayi ta quramai idanu daga bisani tayi murmushi tace you are still the same  itama ta girgixa kanta.Billy I don’t know  what’s going on but xuciya na was telling me something kamar da wani abu I mean kamar something ix wrong,Billy I didn’t expect irin wannan tarbar from you,gaya mani meke faruwa,tsayawarda motarsu tayi ita ta katse xancenda yakeyi,kallonshi takeyi mu shiga daga ciki ta mude motar ta wuce,ga baki daya kanshi ya kwance amma kamar wanda aka yiwa asiri haka shima ya bude motar ya fito,driver kuwa qoqari yakeyi ya bude boot din motar domin ya ciro kayanda ya saka amma da hanxari Usman ya dakatarda shi,xo nan please ba sai ka fitarda kayanba,ya tura hannu al’jihu ya ciro warlet ya qidaya “yan dubu-dubu a qalla xasu kai goma ya danqawa drivern ga wannan ka hau acaba ka koma gida nagode sosai kaji.Wani farin ciki ne ya kamashi ,ji yakeyi kamar ya rungume Usman din akan matuqar dadinda yaji nagode kwarai ranka shi dade Allah ya saka da alkhairi ya qara daukaka da budi,Usman bai jira y agama jin maganganun yabo da jin dadinda yakeyi ba ,ya gyada kai kawai yace amen kana yasa kai yayi cikin gidan.A falo ya tarar da su ga baki daya suna jiran shigowarsa yanda ya gan kowa ya kafe shi da ido ya sanya ya dan tsaya na “yan daqiqu,Hajiya Lara ice ta katse kallon-kallonda akeyi.Bismillah xo ka xauna please murmushi yayi kana ya nemi wuri ya xauna,kafin yayi yunqurin fadin wani abu tuni Tukur yayi gyaran murya ya fara yi masa sannu da xuwa kana ya bayyana mishi irin matuqar farin cikinda sukayi ga baki daya a sana diyar ganinshi da sukayi ,sa’annan ya gabatarda kansa daga bisani kuma ya fede masa daga biri har wutsiya danganeda abinda ke faruwa tun daga batar Sulaiman mijin Bilkisu da kuma shi rashin lafiyar danshi harya xuwa bacewar dan Hajiya Larai namiji daya tilo da takeda shi a duniya harya xuwa inda suke yunqurin xuwa da shirinda sukeyi na ganin qarshen wannan fatalwa tareda yi masa bayanin shi kadai ne xai iya taimakonsu ya gaya musu duk wani abinda yake ganin ya sani danganeda ita wannan fatalwar domin su fara hanya domin can dama rashin ganinsa kawai ya tsayadda su.
       Tsit Usman din yayi kamar wanda ruwa yaci me ma xaice,mema yake ciki,mema yake tunani kwata-kwata ya kasa ganewa ya rasa a sama yake ko a qasa,miqewa yayi ya janyo hannun Bilkisun idanuwansa jajur mu tafi ya fada tareda janyota da qarfi,ina xamuje,tsayawa yayi ya juyo da qarfi because I don’t  have time for this nonsense kuma I’m 100% sure kema haka,kinji wai abinda yake fada wai kinada miji shi xakije nema alhali kuwa gani a tareda ke a yanxu,Billy have u lost it meye haka me kikeyi anan,I didn’t expect you to waste your precious time akan irin wayannan abubuwa,mema kikeyi a kaduna,ya danyi dan guntun tsaki,ki bar wannan maganar kawai meye ma yi a hanya yanxu dai lets go!.Kwace hannunta tayi cikin tsananin fushi ta fara xance;Yes! I lost my mind I lost it hawaye suka fara kwaranyo mata kamar fanfo,kallonshi itama takeyi idan dai xuwa neman mijina ne yasa kake daukana mara hankali na yarda 100% ni mahaukaciya ce.Wani mayen kallo yayi mata No! No! No! ya fada da qarfin gaske a’a ban yard aba ,ban yarda kinada wani miji ba Billy you can do this to me,hawaye suka xubo masa a yayinda ya gani a cikin idanuwanta cewa abinda take fada tsagwaron gaskiya ce.Haba Billy! Haba Billy! Why! Why! Me yasa xakimun haka,I love you with all my life mun yiwa juna alqawari akan ba xamu taba son wani ballantana har muyi aure idan dai bada junanmu ba me yasa xaki karya alqawari me yasa xakimun haka tun a lokacinda mukayi bankwana da juna na tafi ban taba kallon wata mace a matsayin mace ba,kece kadai wacca na sanya a raina  kullum burina da fatana bai wuce naxo na aureki mu wuce tare a gidana ba ki kuwa Haifa mun “yaya kamar yadda muka tsara nida ke,runtse idanu yayi,da sauri kuwa ya  bude idanun sai kuwa idan tilasta miki akayi na tabbata ba xaki iya yimin haka ba,nunfashi ya ajiye har a lokacin hawaye xuba sukeyi daga idanuwansa na tabbatarda tilasta miki akayi idan kuwa ba haka ba,ba yanda xaki auri wani idan dai bani MAN dinky ba.Wani tsakin takaici tayi ta girgixa kai a cikin ranta tana fadin what is wrong whit this guy,sauri yayi ya goge hawayenda ke xuba daga idanuwan nasa,kada ki damu yanxu daga nan a police station xamuje da kuma kafafen yada labarai ,xa’a nemoshi domin yaxo ya sallama kayanda dama can ba mallakinsa bane kayanda ya kwata da qarfi da yaji kasancewar xuwan mai abu.Wasu sababbin hawaye ne suka xubo kwaranyo mata Usman ba wata police station dinda xamuje ina kuma so ka sani ba wanda ya tilasta mani domin nayi wannan auren,auren soyayya ne nayi,ba kuma wanda nakeso da qauna a duk fadin duniyarnan  daya kai mijina,me kake nufi All those years daka share na xauna nayita jiranka for God sake! Nifa macece dan kawai kacemin xaka dawo sai kawai nayita xama ina sauraren xuwan naka,a yaushe ne mukayi da kai xaka dawo after one year! Ta fada da qarfi ko xaka iya lissafa  how many years yanxu da tafiyarda kayi,look at me dan Allah ka kalleni da kyau ka gani I’m all enough ace nayi aure,kana ganin iyayena xasu sakamin ido ne kullum suna kallona a gabansu,and idan suka tambayeni kawai sai nace ina jiran dawowarka ne,I tried nakai kusan 3 to 4 years ina jiran dawowarka,ban kuwa saurari ko wane namiji ba a cikin wayannan shekarun na samu many many proposals but I reject them all,har Allah ya qaddari iyayena suka yimin xabi na alkhairi wato Sulaiman da farko abin yaxo kamar arrenge marriage but later on ya rikida ya koma love marriage,ina sonshi Usman ina matuqar qaunarshi fiyeda komai a duniya xan iyayin komai domin naga na cetoshi daga halinda yake ciki,kuka mai tsanani ya kwace mata hannunta ta axa akan cikinta ta kalleshi I’m pregnant ,kuma cikin na halak ne wanda kuma yake da cikin shine love of my life,bai jira ta kammala xancenda takeyi bay a gyada kai yace thank you,thank you so much Billy I’m greatful ni kike gayawa haka nine kike gaggayawa wayannan maganganun thank you,shima kukan kwace masa yayi cije lebe yayi ya kalleta ga baki daya abubuwanda kika gayamin basu is aba har sai kin dubeni kince na taimaka miki domin nemo mijinki,Billy ban cancanci haka daga gareki ba,share hawayen yayi kana ya murtuqe fuska,idan kece a matsayina xaki iya taimakawa da wani abu domin kawai matata ta dawo,wear my own shoes would you do the same,shiru tayi tana kallonshi  ba tareda ta bashi amsa ba,I guess the answer is No! dan haka nima baxan taba taimakawa ba koda kuwa da komai ne wajen ganin wanda ya tarwatsa rayuwata ya dawo,kama hanya yayi yana yunqurin ficewa abinshi,da gudu Bilkisu ta isa diny ta dauko wata sharbebiyar wuqa,a gabanshi ta tsaya ta bude hannuwanta wanda hakan yake nuni da tana dakatardashi ne,a’a ba xaka wuce haka kawai kai tsaye ba Usman ya xama dole ka idarda abinda ka fara,kaine ka tarwatsa rayuwana nida mijina a sanadiyarka ne mijina ya salwanta duk kaine ka tarwatsamin farin ciki na inaga abinda ya rage ka aikata yanxu shine kaa karbi wannan wuqar ka sokeni da ita ka kawo qarshen rayuwata da duk wani baqin ciki da damuwata ta miqa mishi wuqar karbi! Ka kasheni,shine abu mafi sauqi a gareni da ace ina rayuwa a doron qasa alhali mijina yana a cikin mawuyacin hali kuma kadaice nakeda damar fitarda shi daga wannan halin amma na gaxa akan kawai wani abu daya shiga tsakanina da kai,ka karba nace! Ta buga masa tsawa,ji yakeyi kamar an cire xuciyarsa ne daga jikinsa an jefata a cikin wuta mai matuqar xafi da ruruwa,shi Billy ke gayawa ya kasheta akan kawai yace ba xashi taimaka musu ya fadi musu abinda ya sani dangane da fatalwarda yaji suna fad aba,I cant baxan iya kasheki ba Billy ya fada sannu a hankali,faduwa tayi akan gwuiwowinta roqonshi takeyi cikin tsananin kuka na roqeka Usman ka taimaka mani ka ceto rayuwata data mijina ka taimaka ko domin abinda yake cikina kada idan ya girma ya tambayi ina mahaifinsa na rasa amsarda xan bashi domin baxan iya gayamasa ya bata a sanadiyar wani tsohon saurayina ba kuma kuma tsohon saurayin nawa shine kadai xai iya gaya mana inda xan nemoshi amma ya qi amincewa ya gayamin a sanadiyar ban jira shi yaxo ya aureni naje na auri mahaifin nashi ba,ka taimaka mani ka tausaya manakada gidanmu ya tarwatse na roqeka ka taimakamun dan Allah,ta riqe masa qafa tana sharara kuka mai matuqar ban tausayi a wurin duk wanda yaji.Sauri yayi ya tayarda ita shima kukan yakeyi,Billy kece farin ciki na ki sani xan iyayin komai a duniya domin kawai naga farin cikin ki,ki share hawayenki nayi alqawari baxan tafi ko’ina ba har sai an gano duk inda mijin naki yake a fadin duniya koda kuwa hakan na nuna rasa tau rayuwarne because I can sacrifice my life to depend yours,kince nine na tarwatsa rayuwarku ko,I will be the one to pixed it I promise you,wasu xafafan hawaye suka gangaro masa cikin sheshshekar kuka yake maganar ,a halin yanxu bansan komai dangane da fatalwa ba bansan wata wacca take sona har ta yadda ta kasha kanta a kaina ba wallahi amma nayi alqawarin kowacece xan nemo labarinta da duk wani abu daya shafeta,kuma dani xa’aje har inda xa’aje kamar yadda na gaya miki sai na damqa miki mijinki a hannu is my promise,sa kai yayi da nufin ya ida wucewa,maganarta ne ta dakatar dashi,ina xakaje,xanje na kama Hotel ne ko kuma na sauka gidan abokina,amsar kawai ya wurgo mat aba tareda ya juyo ya kalleta ba,muryar Tukur sukaji a bayansu; inagaxamanka anan gidan xaifi idan mu duka muna a wuri daya xamufi samun qarfin warware duk wata matsala.Juyowa Usman din yayi shi sam ma ya manta da cewar akwai wasu a falon. Hajiya Larai ce ta sakobaki;abinda ya fada gaskiya ne Usman xamanka anan xaifi xamanka a ko’ina muhimmanci,Bilkisu ya kalla ta gyada masa kai alamar tana goyon bayan abinda suka fada,shima gyada kan yayi,Hajiyarce ta nuna masa wani daki ga dakinda xaka xauna a can empty ne ba kowa a ciki amma a kullum sai an gyara shi an tsaftace shi ni kuwa keyin gyaran da kaina domin dakin dana ne daya bata kamar yadda Tukur ya gayama,gyada kai kawai yayi ya nufi hanyar dakin ,tsayawa yayi ya ciro mukullen mota ya miqawa Hajiyar  please ko xaki taimaka ki bawa driver  ya ciromin kayana da suke a boot,amsa tayi ta gyda mishi kai okay.Harya nufi dakin kuma ya sake dakatawa kamar wanda ya tuna wani abu murtuqe fuska yayi ya juyo ya kalli Tukur  sam! Bai yarda dashi ba,meye sunan Alhajinda ya sanya kayi masa aikin ,Alhaji Aliyu wanda kuma aka yiwa aikin….a tattare suka fada lokaci daya shida Usman din ALHAJI UMAR! Ga baki daya wayanda suke a falon suka qura masu ido mamaki ya kama kowannensu hatta shi kanshi Tukur din,cikin tsananin fushi Usman din ke Magana,kai ne axxalumi na farko dana taba gani a duniya duk kai ka janyo wannan abin,ta yaya ma xamu iya yarda da kai ne,ya kafeshi da ido sai huci yakeyi kamar wani namijin kure,wanda ya sanyaka kayi masa danyen aikin ba kowa bane face qanin mahaifina!wanda kuwa akasa ka hallaka shine MAHAIFINA! Biological father dina wanda ya haifeni,kai babban maqiyi nane tunda kuwa nayi arba da kai xuciyana bata aminta da kai ba,ban yarda da kai ba,ka sani idan ma wani abu kake shiryawa to lallai xanyi maganinka,idan kuwa na gano kanasone kayi amfani damu domin cimma wasu manufofinka na can daban xan axabtarda kai xan kuwa tabbatar kayi nadama mara iyaka.Billy ce tayi sauri ta budi baki da nufin Magana amma caraf! Tukur din ya amshe,kada ki hana shi fadan abinda yake ransa yanada daman fadan abinda duk ya gadama kuma koma da wane irin suna ya kirani sam baxan damu ba sai dai inaso ka sani akwai wayanda suka aikata ta’asarda tafi tawa a duniya kuma daga baya suka gano hanyarda suke kai ba mai bullewa bace suka watsarda miyagun ayyukansu suka rungumi kyawawa Allah ta’ala ya shiryarda su ya kuma datarda su suka kasance cikin masu rabo nasan na aikata laifuka a baya amma kuma yanxu na canxa daga mummuna xuwa kyakkyawa,yayi murmushin yaqe komai xan fada nasan baxaka yarda dani bad an haka ba amfanin maganganuna ma,dallah mishi harara Usman yayi kana yasa kai ya nufi dakinda aka nuna mishi ya shiga tareda bankado qofar ya rufe,Duka wayanda suke faloon shiru sukayi Kaman ruwa ya cisu ba wanda yake cewa kowa komai daga bisani kowa ya nufi nashi dakin kai tsaye.Hajiya Lara ice aka bari ita kadai a faloon,sai da ta wanke hawayenda suka wanke mata fuska a dalilin abinda ya faru a gaban idonsu  kana ta kwallawa driver kira da hanxari drivern ya shigo ta umurce shi daya daukowa Usman kayanshi a mota ya kai mishi a dakin khalifah ansawa yayi ya fita a falon da hanxari domin ya cika aikinda aka sashi,harta kama hanya kuwa kamar wacca ta tuna wani abu ta yiwo kiran wadda keyi musu abinci,wata dattijuwa e ta fito da murmushinta,Hajiya gani,munyi baqo ne yanxu dan Allah inaso ki dafa masa wani abu wanda ya dace wanda yayi tafiya ya gaji ace yaci,kin gano ai gyada kai tayi na fahimta ranki ya dade yanxunnan kuwa xa’a gama,yauwa idan kika kammala ki kai masa a wancan dakin ta nuna mata dakinda Usman yake ,to ranki ya dade.Hajiyar tasa kai ta fice ta nufi dakinta.

       A can bangaren Usman kuwa xaunawa yayi akan gado ya fara sheqa kuka mai tsananin gaske ,shi mema amfanin rayuwarsa,me yasa Bilkisu xatayi mishi haka,tamkar a mafarki yake ganin komai kuka kawai yakeyi kamar wani qaramin yaro,wayarshi ce tayi ringin da kyar! Ya iya cirota daga aljihunsa ,sunan abokinshi ya gani a jikin wayar da sauri yayi picking.Wai kana ina har yanxu ban ganka ba ko baka gane drivernda na aiko maka bane,abokin nashi ya fada cikin ba’a,where are you Ashir,Usman ya fada kai tsaye,shiru Ashir din yayi,what is wrong,meke faruwa ne Usman,Ashir ya tambaya da sauri,I just want to see you now Usman ya fada har a lokacin kuka yakeyi ,okay! Okay! A ina xamu hadu,Ashir I cant drive baxan iya tuqi ba a halin yanxu kuma na salami drivern da ka aiko ya daukeni.Ga baki daya abokin nashi ya rikice,kana ina yanxu gayamin yanxu xan iso,one minute bari na miqawa wai ya kwatanta ma wajen ya miqe da sauri ya fita daga cikin dakin,ai kuwa Bilkisu ya hango itama ta bude dakin nata ta fito,sauri yayi ya goge hawayenda ke xuba daga idanunshi,itama hangoshin tayi cak ta tsaya da taga ya nufo inda take gadan-gadan ,miqa mata wayar yayi please ki kwatanta mishi wannan anguwar kallonshi tayi,abokinane inaso ne na ganshi,amsar wayar tayi ta kara a kunnenta sallama ta farayi bata jira ya amsa sallamar ba kai tsaye ta kwatanta mishi gidan yanda xai gane kana ta miqawa Usman din wayar.Kallon-kallo suka riqa yi kowannensu idanuwansa a kumbure  da kuwa kayi arba da idanun xaka fahimci har a lokacin xubarda kwalla sukeyi,sun kusa kai minti biyar suna kallon juna  ba tareda daya daga cikinsu yay i Magana ba,Bilkisu ce tayi sauri ta bude qofar dakin nata ta shiga tareda bankado qofar da sauri ta rufe,kallonta yakeyi har sai da qofar ta rufe sa’annan ya kara wayar a kunnensa, ina jiranka.