HUBBUL YAKIN 2


  

ASIYA SADIQ MACCIDO

(ASIKHAN)



Copyright © Asiya Sadiq 7th March, 2019

Hakkin Mallaka (M) Asiya Sadiq 7th March, 2019



Published in Nigeria by

Sharhamak Computer Ventures

Beside Birnin Kebbi Local Government Secretariat

Kebbi State, Nigeria




Tel: 08113777717


A cikin littafi na daya mun tsaya a:

DAGA CIKIN KASHI NA DAYA 


Shi kuwa Sulaiman tunda ya wuce bai tsaya ko inaba sai a bakin gate din office dinsu, kaf ya tsaya tsam kamar wanda yaga wani dodo, sani ya manta oganshi yayi tafiya, ya tafi wajen wani comfrence da za’ayi a sokoto kuma zasuyi kamar kwana shida zuwa biyar basu dawo ba, to meyasa ma wai bai tuna ba sai a yanzu, wani tsaki yayi mai hade da takaici, said a yayi kamar minti biyar a bakin gate din office din nasu sanna ya tada mashin dinshi ya nufi gidan Alhaji day a basu haya domin ayita takare idan yanada wani gida ya canza musu ko kuwa asan yanda za’ayi kafin nan da zuwan kwanaki shida da oganshi zai dawo ya nemi transfer ya bar gari tun a kan layin gidan Alhajin ya fara ganin dandazon mutane ba adadi har ya iso kofar gidansa, me zai gani ga dukan alamu wani abu akayi ras! Gabansa ya fadi a wurinda shimfida take ya dire takalma yayi sallama ya mike hannu tabbas gaisuwar rasuwa ake yayi gaisawa aka ansa masa ya nemi ya gana da babban dansa, kasan cewar yasan sulaiman domin tare dashi akayi process din gidansu Sulaiman. Bayan da Sulaiman ya kara yi masa gaisuwa ya tambayeshi yanda haka ta faru, ya shaida mai matukar rudarwa, a jiya da dare ne yana bacci sai kawai akaga ya mike tsaye ya sauka daga kan gado, ya farayin da baya-dabaya yana ta ko’ina har ya fadi kasa, likitoci sun auna sun fada cewa sakamakon ganin wani mummunan tashin hankali da idon dan adam da kuma kwakwakwar sa basa iya dauka da yayi shiya hifar masa da wani matsanancin bugun zuciya da har yayi sanadiyar rasa rayuwarsa a nan take dirshan ya fadi a kasa hawaye suka riqa zuba a idanuwansa, al’amarinda yayi matukar bawa mutanenda ke wurin mamaki kenan hade da tausayin musamman babban dan Alhaji, lallashin shi aka dingayi har ya dawo cikin hankalishi ya daina kukan da yake. Shi kadai yasan abinda yakewa kuka tabbas shakkah babu akwai wani mummunan abu dake shirin faruwa dasu, gashi sub a yan gari ba yaya zai yi. Ya zabura ya mike ya sake gaisuwa yayi sallama ya wuce, dole subar garinan gobe-gobe ba domin sko yanzu lokaci ya kure musu bad a sun bar garin a yau, kara gudu yayi kamar wanda zai tashi sama domin kar dai wani abu yazo ya sameta domin kuwa Bilkisu shi c eta fado mishi a rai, kar dai wani abu yazo ya sameta. Krar shit ta dawo masa da hankalin shi daga tunaninda yakeyi bai yi ni yar ya dauka ba kuma dai yaji bari ya dauka aljihu ya zara wayar shi sanan abakinshi Nuhu ya gani da sauri ya dayka ya karakan kunnensa, slamu alaikum ya fadawa alaikussalam, Sulaiman don Allah kayi hakuri kaga ban samu dammar kawo su uUmmi ba Wallahi jiya da sakiyar dare mamansu ta kuma da matsanancin ciwon ciki amai da gudawa tun sa’annan muna asibiti sai yanzu muka dawo, yanzu dai Alhamdulillahi ta samu sauki sosai, kayi hakuri fatun sannan ban masan ida wayana yake ba sai yanzu da muka dawo bare na kiraka na gagayama bazan samu dammar kawo su ummi ba kasan ya yanda al’amuran suke wallahi tun sannan bansamu nutsuwa ba sai fa yanzu da kaga na kiraka. Rasa ta cewa yayi can ya lalibo kalamai yace ai badamuwa Nuhu Allah dai ya bata lafiya ya tashi kafadarta sai munzo dubata nida Uwargidata tau amen, amee, Sulaiman, When sai kunzo, sai an jima ya katse wayar. Wani matsanancin gudu yakeyi kamar ranshi zai fiita ya nufaci gidanshi haiqan dearest!dearest! dearest! Yake fadi kamar wani mahaukaci, da karfi yasha kwanar gidansi, kicibis! Yayi da wani abin ban mamaki, Bilkisu ya hango tana fama dariya tana bye-bye da hannunta, kyar ya iso a gabanta, murmushi tayi ta nufaci inda yake sannu da zuwa ga baki daya ta jagula masa lissafi zauwa ke dawa kike bye-bye haka? Malam mu shiga daga ciki ai ko, biye kawai yake da ita, suka shiga cikin gida su waye suka zo wurinki ne haka, ni fah da farko duk kin tsoratani n zata ko ke kadaice a gidan duk hankalina ya tashi, wani kallo tayi mai alamar ina ma fushi da kai, eh ai dole kace haka ai, ta wani shagwabe murya sanna tace stunda kasan Nuhu ya kawo su Ummi! Shine ka tafi abinka ka shallake, to sune nakewa bye-bye da yazo daukan su, nayi-nayi ya jiraka amma yaki ta, su ummi!! Kuma Nuhun ne yazo daukan su!! Mikewa yayi inna lillahi wa inna  illaihi raji’un, a firgice itama ta mike hakika sulaiman dinta ba karamar razana yayi ba to muje na razana a cikin abinda ta fada. Lafiya dearest meya faru meye don Allah gayamin, Bilkisu tashi ki had kayanki gobe-gobe zamubar garinnan, me ya faru ka gayamin! Ta daka masa tsawa tana mai zubarda kwallah batareda tasan ma tayi ba, da kyar ya kwantarda hankalinshi ya zaunarda ita kana ya bayyana mata duk abinda ya faru tun daga farko har rasuwar Alhaji da rashi lafiyar mata Nuhu duka ya bayyana mata shiru tayi ta kasa koda motsa dan yatsan ta akan tsananin firgitarda tayi Bilkisu! Bilkisu! Ga baki daya batajin abinda yake fada, said a ya wujijigata da karfi sanna ta dawo ayyacinta, Bilkisu karki damu gobe-gobe zamu bar garinan a’a ba sai na ta fada tana mai fashewa da matsanancin kuka, a’a Bilkisu ki bari gobe tunda sassafe, a’a ta durkusa kasa ta rike masa guwayyunsa na rokka don Allah Mubargarin nan a yau din nan, nunfashi ya aje, to shikenan jeki hado kayanki mu wuce, karki damu sa sauran kayan, idan nazo karbar transfer letter din azan wuce dasaura, shiga tayi ta tattara kayanta shima tattara nashi kayan yakeyi, sai a yanzu ta gane lallai wayannan basu Ummmi bane, bayan da ta zuba maganin sai taga duk sun wani kamar rikice, ta tuna sanda ta aika amina kitechen ta dauko mata plate sam takasa shiga a kitchen din, sa yanzu ta fahimci tun lokacinda ta zuba maganin basu sake takawa daga cikin falon ba. Tsam ta mike tunawa tayi da yanda Ummi ta dauko jug a cikin feeg wanda ta cika da drinks din kwakwa ta wankada akan kofar fita falon wanda zata fitar da mutum zuwa ta gane da gangan ta fadi ta zubar da drinks din don dai kawai su samu su fita. Kamala hada kayan tayi a dai-dai lokacinda shima y agama kamala nashi muje ko yace ta janyo hijabinta data ajiye kalar kayanda ta saka tace eh, muje tare suka nufi hanyar fita, tsayawa sulaiman yayi ya kalli gidan da kyau ya gayda kai ya wuce suka kulle gida sun juya zasu wuce sukaji an kyalkayale da wata mahaukaciyar dariya, duban juna kawai sukayi ba tareda sun ce ko kalaba sukaja akwatunansu sai a kan titi suka tsaya, wani mai a daidaita suka tsayar, garge zaka kaimu, yasa kayansu ya nufaci garge din, misalign karfe uku da rabi ne narana garin ana tsananin zafi, wurin fifa ya tsayar day an layin su, jira suke ya dauko musu hannu su wuce, ji tayi kamar ana girgiza kasa, ruguzum komi na wurin ya fara rusgawa cikin kasa, kuwwa da hrgowar jama’a kawai kakeji, motuna da baburra sairuguzawa sukeyi kamar an cilla a dai daita sahu su, sulaiman ya runtuma cikin, caf tasa hannuwanta ta cafkoshi, wani irin tashin hankali mara misaltuwa ta shiga kuka take tana hargowa karka tafi ka barni tana rike da hannunshi sauran jikinshi kuwa yana lib, hannunshi ya fara subuce mata tana mai tsala uwar kuwa tsundum ya fada yana kiiran sunanta Bilkisu! Bilkisu! Sulaiman ya ingi zata, caraf ta dawo daga wanna mummunan mafarki zatace ko tunani, ita dai tasan a zahiri taga wannan abu ya faru, lafiya me kike tunani haka? Sulaiman ya katseta, waige-waige take da idanuwata cikin mawuyacin hali, ke meye? Meya faru? Jin ta kama hannuwanshi ta jinike da nata, a jiyar zuciya yayi, karki damu masoyiyata insha Allahu zamu isa gida lafiya, gobe irin wannan lokacin kina gaban Umma, ya fada yana zolayata, duk day a kokarin da tayi wajen gani tayi murmushi ta kishingida dai-dai wajen ‘yanBauchi aka ajiye su, sune passengers na farko da suka fara loda a motar, bayan an saka masu kaya a mota, suka shiga ciki mota suka zauna suna jiran zuwan sauran passengers, zaunawar su keda wuya dum! Sukaji ko ina yayi rufe da wani matsanancin duhu smai tsananin muryoyi sukaji kala-kala ta yadda ba zasu iya tantance ko murya mace, namiji? Ko kuwa karamin yaro ba. Gargadinsu a kayi da murya mai kaushi akan suyi gaggawar fita daga cikin motar na su koma ya zuwa gidansu da suka baro, muddin kuwa sukace zasuyi taurin kai, kuwa zasu hadu da matsanancin hadarin motar da zatayi sanadin halkar duk wani passenger da ke a cikin motar, sanna kuma aka wayanda basuji basu gani ba, domin kuwa driver matarshi ta haihu kwana biyu yayi saura ayi biki, idan sukayi sanadiyar mutuwar wazai dauki nauyin iyalishi kuwa wanda yake kan gaba a kusa da driver dan makarantane shi kadai ne namiji a gidan su, mahaifinsa ya rasu mahaifiyarsa ke wahala wajen ganin ta biya masa kudin makaranta. Ita kuwa wannan matar ‘yaranta duka biyu marayu ne ‘yan uwan mahaifinsu sun kwace musu dukiyarsu, wajen ‘yan uwanta zataje neman agaji. A haka akaci gaba da lissafo musu ko wane passenger da abinda yake kunshe dashi duk domin dai so fita daga cikin motar bayanta aka gama gargadinsu, wayau! Sukaga ko’ina ya yaye, kuma motar da suke ciki hart a cika da passengers, kamar yadda aka shaida musu haka kuwa suka gani, duk wayanda aka lissafa musu a motar su da ne ke ciki. Kallon juna sukayi ba yareda sun samu dammar furta wata kalam ba, wayar direba ce yita wau kara, dauka yayi tareda sallama, slamu alaikum lafiya kalau wallahi, a’a alhamdulillahi mun gode Allah, amen, amen, sosa kunnenshi yayi yana ‘yar dariya, eh saura kwana biyu ma ayi bikin ai ina Allah ya yarda. Dam gabansu yafadi suka sake duban juna da karfi, tare suka hada baki dakata!! Duk motar kowa ya jiyo ya ba, ana saka kayane a but da hanzari suka bade murfin motar suka fito, mun fasa tafiya Sulaiman yace gaywa condester, don Allah kuyi hakuri wallahi mun fasa tafiyar me kace malam, kamar ya ya kunfasa lafiya wanna aima maganar banzace, duka mutanen wurin suka taso wasu na bayadda hakuri wasu na zugawa, anan dai aka samu wani dattijo mai hankali da sanin ya kamata, yace tunda ai ga wasu passengers nan ba sai kawai su shiga a madadin wayannan ba, ai wannan abun bai kai na wani dogon bayani ba, sukayi masa godiya suka nemi a dai-daita sahu suka sake saka kayansu suka nufi gidansu da suka saka baro, suka bar mutanen garage din kowa tana mamakin wayannan mutane haka, su kadai suka san dalilin da yasa suka bar motar, ba kuzari mai adai-daita ya sauke su a kofar gidansu, said a suka yi kamar minti bakwai a tsaye suna kallonn-kallo sanna Sulaiman ya bude gida suka dunguma a ciki, ga baki daya duniya tayi masu zafi komai ya kulle musu, sun ma rasa ta inda zasu fara bamai cewa kowa ko kala, suka isa bakin kofar falo ya saka key a ciki yana kokarin mirdawa ya bude kofar falon, kiririn,kirin wayar Sulaiman tayi kara su duka suka zabura da karfi, hannu yakai aljihu ya ciro wayar, sunan mahaifinshi ya gani ya bayyana a gaban screen din wayar shi, dauka yayi, yayi kokarin boye duk wata damuwar shi, da ke tattare dahshi, slamu alaikum Abba ina wuni lafiya kalau, lafiya kalau take, komai Alhamdulillahi, Na’am Abba na nameye ya tambaya yana mai nuna mutukar mamakinshi a filli kamar a gaban Abban nasa yake, kallonta yayi da hanzari eh yayi murmushin yake yace amen, har yanzu kallonta yake yi, to amen baba ehan, ya katse wayar har yanzu kallonta yakeyi, ga baki daya hankalin shi a tashe yake itama kallon nashi take yi, meye ta tambaya tana kallonshi wai Abbane yake tayani murya, wai a dazun nan Ummata ta kira ki a waya, kika gaya mata mun dawo ne daga Asibiti likita ya tabbatar mana da cewwa kinda juna biyu na tsawon wata biyu, dirshan ta fadi zaune barkewa tayi da wani matsanancin kuka, shima, sulaiman zama yayi a dai-dai kusa da ita sai dai wannan karon ba lallashinta yakeyi ba, hada tagumi yayi ta fada kogon tunani, shi ba abinya fada ta gida ba, a can hankalin su ya tashi, kuma ma zai iya yuwa idan wani yace zaizo a kasheshi a kan hanya sunfi minti goma anan zaune, sa’annan Sulaiman ya mike ya iyadda bude kofar falon su duka suka shiga ciki, jawo akwati takeyi itama suka nufi daki ji tayi kamar an ja mata kafa jicce ta fadi kass ram! Yunkurawa tayi ta tashi amma ta kasa, wasu taurarin wahala ta ringa gani sunayi mata yawo, yarda tashi akwatin yayi ya nufo inda take da gudu, yanka kokarin tada ta, lumshe idanuwanta ta farayi, tun tana iya budsu har takai ga duka suka rufe rungumeta yayi ya kwala uwar ihu, da hanzari ya tallabeta da gudu ya fito baima tsaya ta wani rufe gida ba. Mijin Khadija yayi kicibis dashi ya dawo, da karfi ya tsayadda mota, Sulaiman da gudu ya shiga, Asibiti, asibiti! Da isarsu asibiti aka daurata saman keke da gudu aka wuce da ita emergency, gaf aka rufe kofar emergency aka dakatar dashi daga yunkurin shiga cikin dakin da yayi, jiginawa yayi a jikin bango emergency zaune yayi a nan wurin ya fara kuka ne ya ringa lallashi da kyar da sidin goshin daina hargowarda yake ya zama hawaye kawai ke zuba daga idanunsa, nurse c eta fito da fara’arta da kafri suka mike su duka sister ya lafiyar jikinta, zan iya shiga yanzu, don Allah ku bari na shiga nag anta, Sulaiman k eke jero wayannan zancen duk shankalinshi a tashe relax malam cogratutaltion ma, wani kallo yake mata me kikace? Cewa nayi congratulation matarka na dauke da JUNA BIYYU na tsawon wata biyo, kuma zaka iya shiga ka ganta, za ma kaiya tafiya da ita, because she is out of danger known. Bai jira ta kommala jawabinta ba yaruga da gudu zuwa cikin inda dearest dinshi take, zaune ya taradda ita tana kallon yan yatsunta tsaye ya tsaya cak, kamar tasan dashi ta daga kai suka hada ido, ya karaso inda take ya rungumeta yana zubarda kwalla, Alhamdulillahi kin tsoratani, don sAllah kada ki sake yimin irin haka. A nan aka sallame su daga asibiti maigidansu Khadija ya maidasu gida, sukayi masa godiya sun ma rasa zaune kawai sukayi kamar masu ansar gaisuwa, kiran mariba akayi, suka tashi sukayi alwala, ya jagoranceta sukayi sallah, mikewa yayi ya fada kichen a dafa mata indomies, a wani bangare na rayuwarshi harga Allah dadi yakeji mara misaltuwa, matarshi nada ciki, kenan zai zama baba, zubo indomie yayi a flate ya kawo masu a nan bedroom dinsu tareda rowan da zasu sha, aka kira isha’I suka mike suka sauke farali, suka jawo kwanon abinci sukaci sukasha ruwa, ta tashi da dauki kwanuka da ni yar ta kai kitchen karaf ya amshe, no wannan ba aikin ki bane yanzu, zauna ki huta, kada ki wahaltamin da baby, duk da irin halin da suke ciki said a tayi yar dariya, duk kunya ta lullubeta, ya dauki kwanuka yaje ya ajiye ya dawo, suka yi addu’a suka kwanta. Wayyo!! Wata kara aka buga mai mai matukar firgitarwa zunbur suka sauka daga kan gaso jan abu sukaji anayi a falo, kasan tys idan ana jan abu akanshi zai ringa bada wani sauti daban, kuka sukeji anayi matsananci, a hankali suka tattaka ya zuwa bakin kofar daki yaddazasu iya hango abinda ke faruwa a falon, da baya sukaja da kafri saka makon ganin wanan tashin hankali da basu taba gani shi ba, wata mace ce ko ince budurwa wace bata wuce shekara goma sha takwas zuwa sha tara ba, ake ja, batareda suna ganin mai jan nata bag a baki daya jikinta jinine faca-faca, kama kuwa kadan ya rage ya rabuda gangar jikinta, rokonsu take tana kuka don Allah ku taimaka mini, karaja sukeyi da baya suka rungume juna suka kankame waje daya, wuf tayi ta nufo su da niyar ta cafke su, kamar an wulla ta ta fada can gefe daya, sake mikewa tayi kanta yana shillo ta kara nufo su amma kamar a karon farko ma sake wurgata akayi, kuwa take kala-kala iri-iri tana yunkurin kamasu amma ta kasa, su kuwa suka buga suka kara ja da baya suncakankame juna, duk wani yunkuri, na shiga cikin dakin tayi amma ta kasa Sulaiman ne yayi karfin hali ya ja kofar daki ya rufa da karfi ya dawo daga baya. Duk hargowarda takeyi a kunnuwansu yake, addu’a suka yi suka tottafa ko’ina suka haye kan gado ko runtsawa ba wanda yayi-sai yanzu Bilkisu ta gano dalilin da yasa ta kasa shigawa acikin dakin, maganinda baban nan ya btane, haka suka zauna ba wanda ya koda runtsa idanuwashi, sai a shiyoyin asuba su duka bacci ya sace sub a tareda sun sani ba Sulaiman ya fara falkawa, kasa rufe bakinsa yayi sakamakon kashin ganin matarshi da yayi akan gado, kofa ya gani bude, a hankali ya tashi ya fara tafiya yana duba kofar, can ya hango Bilkisushi a falo zauna murmushi, zo dearet, zo mu karanta Qur’ani kama meye yayi kadan ya cuta mana, shi nake karantawa kazoo mu sauke Qur’ani a yau dinna, ajiyar zuciya yayi ya sauke nunfashi da karfi okay bari na dauko nawa Qur’anin, a’a ai gashi na dauko duka zo kawai mu karanta, fitowa yayi ya nufa ci falon ya tsallaka ya fada cikin falon, sai dai kuwa abinda bai saniba Bilkisunshi tana kwance sa bias gado tana sharer bacci abinta. Sai da gari ya fara wayewa sannan ta farka itama kamar yadda Sulaiman yayi haka itama ta fara duban mijinta har a toilet ta dubashi bata ganshi ba cak ta tsaya da taga kofa a bude, a hankali ta fara tafiya ta nufaci kofar da zata kaita falo wani faduwar gaba taji da bugun zuciya tsallako kofar tayi ta nufo mijina kam ta kame tsaye akan matsanancin tashin hankalin da taji, mijinta dearest dinta ta gani a zaune da wasu kananan kayan da hula da wasu rufaffun takalma kai! Sak shigar USMAN! Yadda yake zama, yadda yake kada kafa daya juye hularda yake yi kai! Kome sak na MAN! Daga kai yayi ya fara dubanta tun daga sama har kasa, itama suban nashi takeyi, nikewa yayi kau!! Ya wanka mata wani hatsa bibin mari said a ta fadi ta fasa bakin ta, kamar wanda ya dawo daga hayyacinsa y ace cikin wata murya wadda ko ba’a gaya maka ba kasan mace c eke wannan murya, yanzu idan Usman yaji yanda nayi miki fa ya fara dube-dube kamar wanda yaga usman din a falon, da karfi kuma ya juyo ya kalleta kallo irin na mugunta da tsananin kiyayya yaci gaba da Magana wannan dai ta mata, idan na kasha ki ai bai zai taba sani ba yana fadi yana cize hakoranshi, ya nufaci inda take ya sa hannun ya cafko wuyanta ya dagata dashi sama har ya cirata har karfi aka banko kofar shigowa falon! Tsohon nan ne da suka saba dashi, da karfi ya wankada mashin wasu ruwa da suke rike da hannunshi, wai gowa Sulaiman din yayi da karfi suka hada ido da tsohon, wurgarda Bilkisu yayi da karfi ya sheka ya nufi bangon falo tuma yayi ya tsunduma cikin bandon baya bace. Baban yaje ya tayadda ita kuka takeyi kamar ranta zai fita, ba dai Usman ne keyin duk wannan abinda ke faruwa ba, take fadi tana kuka mai tsanani. Ba Usman bane ke muku wanna abun amma sanadiyar sa ne duk wannan abun ke faruwa, how? Tayaya? Ina mijina kuma wane sanadine na Usman aka da yake faruwa dan haka ta fada tareda zubewa a kasa tana kuka. Gyara zama yayi ya fara fadi mata kamar haka --------

        Ku biyoni a littafi na biyu dan jin cigaban kayatacce labari.

Taku mai debe muku kewa Asiya Sadiq Maccido
(Asikhan)

 
Hubbul Yaqeen Book 2 Complete
Da farko dai sunana Tukur a “yan shekarun da suka gabata ba nida wata sana`a data wuce bokanci,na kasance hatsabibin boka wanda yayi shura wajen aikata miyagun aiyuka daban-daban.Xaro idanuwana tayi cikin tsoro da tsananin mamaki,bai damu da yanayinda yaga ta shiga ba dama can yasan dole hakan ta kasance,ci gaba yayi da labarinda yakeyi kai tsaye kamar wanda ya tunanao wani abu mai matuqar bacin rai da baqin ciki yace duka cikin sharrukana da muguntana ban taba cin karo da wani abu daya dagulamin lissafi ba sai kuwa sharrinda nayi na qarshe,lokacinda nake aikina sam!banajin wani tsoro ko fargaba,bammasan meye hakanan ba a rayuwata.Manya-manyan masu kudi da jigajigan  yan siyasa hadi da tururuwar tulin mata kullum basa katsewa a dan qaramin gidana duk kuwa wanda nayiwa aiki ina mai tabbatar miki da sai ya godemin acikin muguwar sana`arda nakeyi a watarana na aikata wani hatsabibin aiki wanda nake dana sanin aikatashi a yanxu,tun bayanda na aikata wannan aiki ban sake samun kwanciyar hankali ba.Bari na fayyace miki yadda xaki fahimta,a wata rana wani hamshaqin mai kudi yaxo ya sameni ya gayamin damuwarsa da kuma irin maganinda yake buqata,ya gayamin cewa su biyu kawai iyayensu suka Haifa a duniya shida yayanshi .Yayan nashi kuwa ya kasance mutum mai sa`a da nasara sosai,kasuwancinsu da komai nasu daya amma dukda haka yayanshi ya fishi arxiki da dumbim kudi,yabi ko wace hanya da yasan xai iya bi amma tamkar ingixa dukiyar yayan nashi yakeyi wannan abin yana damunshi matuqa,ana cikin haka sai Allah yayiwa matar yayan nashi rasuwa,daya daga cikin abokananshi ya bashi auren `yarsa mai matuqar kyau mara misaltuwa ya gayamini shifa tunda ya daga idanu yaga wannan matar ta yayanshi to kuwa bai sake samun nutsuwa ba,abin duniya duka ya dameshi yayanshi ya xame masa qadaren bakin tuli dan haka yaxone yana buqatar a kasha yayan nashi,kuma yanaso duka dukiyar yayan nashi ta dawo mallakinsa kuma ya aure amaryarsa kar kuwa a samu wanda xaiyi Magana ko a danginsu ko abokanen yayanshi har abada,tareda yaimin alqawarin idan nayi masa wannan aikin xai bani makudan kudadenda ko a mafarki bait aba ganin irinsu ba.Banyi mamaki ba domin sharri kala-kala ba irin wand aba`a kawomini ba,na amsa da wanna shi yafi komai sauqi a wurina.Na fada bakin aikina gadan-gadan ,bincike ya nunamin dole nixan binne sharrin da hannuna ,a kuwa gidan shi wanda xa`a yiwa aikin,wannan sam  bai dameni ba domin xan iya shiga na binne abin harna fito ba tareda wani bil`ada ya ji boka
duba kyakkyawar yarinya ta fito daga cikin gidannan naku a firgice tana riqeda wuqa jina-jina,a cikin firgici ta miqamin wuqar qin amsa nayi na kuwa ja baya,kuka ta fashe dashi kana ta duqa akan gwiwowintw na roqeka dan Allah kwa karbi wannan wuqar ka kasheni bana buqatar rayuwa ko wace  irice,ka kasheni kayi tafiyarka ba wanda xai sani dan Allah ka taimaka mani,meye amfanin rayuwana bata jira nace komai ba ta miqe da sauri  daga wuqar tayi da nufin  ta soke kanta cara!na riqeta nidama nake neman inda xan samu sassan mutum sai gashi a bagas! Haka karaka kuskura ki kasha kanki diyata me yayai xafi haka da har kike qoqarin kasha kanki,saannan me kika aikata a ciki ta yaya naga wuqarki da jinni haka kamar wata wadda tayi kisan kai.Banjira  na bata wani lokaci ba nayi mata dabaru irin namu na hatsabiban bokaye na wuce da ita a gidana,ta nunami sam ita batason rayuwarta a lokacin kuwa naga hakan gabaki daya xuciyarta a bushe take,na gayamata ni boka ne akwai wani taimako daxan iya yi mata a matsyina na mugun mutum.Haqiqa xan kasheki kaman yadda kika buqata amma xan tayarda RUHINKI domin daukan fansa a wurin wanda ya quntata miki,xan tayadda ruhinki domin xuciyata na gayamin kina buqatar hajka kuma shi kadai ne taimakonda xan iya yi miki wannan shine karo na farko danaji tausayin wani a rayuwana kuma idan na duba wani gefen kin taimaka mani,bata samu daman bani amsa ba kallona kawai takeyi,dama nasan dama can ba xata gano inda na dos aba,a taqaice dai nina kasheta da hannu na sa`annan kuwa na debe abinda nakeso,bayan na kamala aikina sai na balle qirjinta na ciro xuci yarta na hada da wasu baqaqen magunguna nayi tsafi kana na saka a cikin wata “yar qaramar akwatin qarfe,tafiya nayi mai dumbin nisa a can a cikin duhuwar daji a qarqashin wata qatuwar bishiyar tsamiya wadda take dauke da miyagun al`janu da ifiritai na binne.Dariyar mugunta na riqa kyakyatawa a wannan lokacin tareda jinjina wa kaina dana kasance mutum mafi mugunta da hadari a duniya,sai dai kuwa abinda ban saniba shine na janyowa kaina bala`i da masifa ne bayanda na kamala duka aikina nayi nasarar tayarda ruhin wannan yarin ya wadda ta gayamin sunanta MARYAMA,fatalwarta ta tashi kai tsaye sai dai shi wanda nayiwa aiki wato Alhaji sam bamyi nasara ba domin aikinda nayi bansan yanda akayi bay a fada kanshi yam utu a maimakon yayan nashi.Na shiga rudani sosai domin wanna shine karo na farko dana tabayin aiki ya jagule mani musamman ma bayanda na tabbata aikina na gudanarda shi yadda ya kamata,to amma ba daga nan abin ayake bat un bayanda na aikata wannan danyen aikin nawa mukayi bankwana da kwanciyar hankali ma`ana tun daga wannan ranar ban sake samun kwanciyar hankali ba,kullum  cikin fargaba nike da tashin hankali,tsoro kuwa dashi nake kwana dashi nake tashi.Tun bayanda  Alhaji ya mutu ake axabtar dani,idan kuwa na kwanta da sunan  nayi bacci na kanyi mugayen mafarkai,wani sa`i nakanga  Alhaji ya biyoni da wuqa yanaso ya yanka ni wani sai kuwa yana dukana idan kuwa na farka ga baki daya sai jikina ya riqamin ciwo kamar wanda aka doka a xahiri,wani sai kuwa na kanyi mafarki ya shaqure ni idan kuwa na farka xamji wuyana yana yimin matsanancin ciwo,wani sa`i yakan bayyana a madubin tsafina yana mai hararana wasu lokuta kuwa har a bayim yake fitomin ba,duk wannan ba shine tashin hankalin ba,na kasance inada da kwaya daya talon a duniya na kuwa nisanta shi daga duniyar mugunta da  xaluncinda nake aikatawa,ina matuqar qaunarsa fiyeda komai a duniya,na sakashi a makarantar xamani domin inada mafarki cewa ya xama wani babban mutum a duniya ga baki daya dukiyata shi nake kashewa gashi kuwa yanada matuqar ilimi a qarshe na biya masa kudi yaje qasar waje domin karatu.Ga baki daya baya qaunar sana`arda nakeyi amma yana matuqar gurmamani a rayuwarsa,ina cikin wannnan halin ne kwatsam! Sai wata rana naga ya dawo gida ba a lokacinda ya saba dawowa ba,dukda yake nayi farin ciki sosai da ganinsa amma kuma nayi mamakin ganin nashi,bayanda aka kawo masa abinci yaci muka kebe dashi,yake gayamin gashi ya dawo menene wannan abin da yakeda muhimmanci sosai da har ya sanya nace ya dawo gida Nigeri`a,nayi matuqar mamaki dajin batunsa domin nidai a sanina bamuyi Magana kwatan kwacin wadda ya fad aba mamaki ga baki daya ya rufe ni a yayinda yake tabbatar mani lalla a lalla nine na kirashi nace yaxo da gaggawa ina nemansa,tashi yayi kyam!baba please bari na shiga bayi na dawo,ya barni xaun e cikin al`ajabi da mamaki kuwarsa kawai naji acan cikin bayinda ya shiga koda na runtuma na shiga ciki na taradda shi kwance a qasa magashiyan ko motsi bayayi hankalina  gabaki daya ya tashi abubuwa suka bdaqule mani na rasa inda xansa kaina,a yayinda na shiga halwar tsafina na gano kuskurena  shi dai wanda nayiwa maganin ya kasance ya gaji wani littafine daga wurin mahaifinsa wanda ya qunshi duk wani sirri namu na bokaye tareda adduo`I  wayanda komai hatsabibancin boka  aikinsa ba xayab taba tasirin a kansa ba  a maimakon aikin yayi tasiri a gareshi to kuwa xai koma a wurin wanda ya qulla sharrin,shi qaninsa daya kawo aikin ya rigada ya girba abinda ya shuka saura ni,a dalilin hakane ya fada kan dana,a yayainada ya kawo nan a xancensa sai hawaye masu xafi suka kwarara daga idanuwansa kana ya girgixa kai wanda yake nuna alamar tsintsar nadama hadi da dana sanin abinda ya aikata,kai tsaye ya ci gaba da labarinshi nayi iya bakin qoqarina na binciko hanya daya kacal xa`a bi wajen maganin wannan abin itace na tone abinda na binne kana na lalata aikinda nayi.Na dauka abin yanada sauki amma kuwa nayi babban kuskure,domin bayanda na binciko amsar matsalata ban tsaya bata lokaci ba kai tsaye dajinnan na dosa banyi wani a cikin dajin ba kwasam!fatalwar yarinyarnan na gani a gaba na,tsawa ta dakamin kai tsinannen tsoho! Me kake shirin aikatawa ta fada cikin taqama da Gadara kanasone kaje ka tarwatsani ka shafeni daga doron qasa domin biyan buqatarka.Da farko na xata xan iya maganinta amma wani abin mamaki shine tanada wani hatsabibin qarfi wanda tun a tarihin duniya banji wata fatalwa dashi ba.Haqiqa na tayadda mugun abu,na tayadda abu mafi hatsari a duniya,abinda yaxo ya gagari ni kaina ga baki daya hana tayi kona isa kusada inda na rufe tsafina domin kuwa tanada masaniyar da xarar na tone abinda na binne to ba maganinda nayiwa Alhaji kadai ba hatta maganinda  nayiwa ita kanta xai tarwatse a nan take  naci bone sosai domin kuwa ta axabtar dani da mafi munin axaba ta karairayamin qafafu taji mani raunin a ko`ina a jikina kana ta wurgar dani da kyar Allah ya qaddari na rayu,bayanda nayi jinya mai tsanani,tun kuwa bayanda na samu na warke nake bibiyar wannan gida naku nake kuwa jiran xuwanku,domin kuwa alokacinda take axabtar dani naji tana fadan ba wanda ya isa yaga qarshenta dolene ta dauki fansa da mafi  munin axaba da uquba wadda ba`a taba samu wani yayi ba tun kuwa sa`adda aka kafa duniya,lokaci qanqani ya rage xataxo kamar  yadda na tsar aba makawa sai ta xauna a cikin gidana kana ta kwarara ihi mai tsanani sa`annan tacim gaba da xancenta Billy! Billy!Billy! har sau uku saina hukuntaki,saina sanya rayuwarki mafi muni fiyeda wuta kece kika kwacemin Usman daga hannuna ba xakiji dadi ba har qarshen rayuwarki,sai kinsha axabata kana daga qarshe na kasheki da mafi munin kisa  sa`annan ta juyo ta kalleni da qarfi idan ka sake yunqurin xuwa nan sai na kasha duka danginka daga qarshe kaima na kasheka kuma ka sani ba kai kadai ba ma duk wani mahaluqinda yayi yunqurin xuwa wannan dajin domin ya kawar dani daga doron qasa tamkar yana sayen mutuwane da kudinshi,duk wani wanda ya shigo wannan jejin xanji ta bushe da matsananciyar dariya kana ta bace bat! Dogon numfashi ya saki kana ya dubi Bilkisun dan Allah kada ki kalleni a mtsayin axxalumi ki kalleni a matsayin wanda yayi kuskure a baya kuma ya gyara kurensa ya tuba ya xama mutumin kirki wanda yake qoqarin gyara kuskurensa koda xai rasa rayuwarsa la`allay a samun rahama a wurin ubangijinsa. kafeshi tayi da idanu  kallonshi takeyi cikin tsananin tsoro da mamaki bude baki tayi domin tayi Magana amma ga baki daya rasa me xata ce tayi wani rudani ta shiga mai tsanani daga bisani ta fashe da matsanancin kuka main sosa xuciyar duk wani mai saurare,rarrashinta ya shiga yi Bilkisu yanxu ba lokacin kuka bane lokacine daya kamata ace kinyi damara domin yaqar wannan axxalumar ki tuna mijinki,kuka bashi xai dawo mikim dashi ba dolene mu yaqi wannan fatalwar domin ceto rayukan masoyanmu kamar wacca ta tuna wani abu jijjiga kanta tayi alamar Eh! Kana ta goge hawayenda ke xuba daga idanunta kana ta qura masa idanu alamar kai nake saurare,Bilkisu inaso ki gayamin komai da kika sani dangane da wannan fatlwar domin kuwa ba xamu taba samun nasara a kanta ba har sai mun san komai dangane da ita,matsawar kanaso kayi nasara akan abu ko menene sharadi na farko shine kasan wannan abin ciki da waje idan kasan komai dangane da abin to shi yake baka tabbacin xaka iya yaqar abin,sai dai ita nasara a wurin ubangiji  take Allah(S.W.T)kuwa yana bayan duk wani mai gaskiya,meya hadaki da wannan fatalwar,ta yaya akayi kika kwace mata saurayi,wanene usman,duk inaso na sani.Bansan ko wacece ba ban taba kwacewa kowa saurayi ba hasalima ban taba xuwa kaduna ba sai a wannan karon da aiki ya kawo miji na anan ni ban santa ba bansan me yasa takeso ta quntata mini ba,kamar wacca ta tuna wani abu ta juyo da qarfi tace nasan usman.Usman tsohon saurayinane tun kamma na haduda mijina munyi soyayya dashi lokacin ina makaranta kwasam! Wata rana yaxo ya gayamin tafiya ta kamashi kuma bai gayamin ko xuwa ina bane tun sa`adda ya wuce kuwa ban qaraji daga gareshi ba bai sake dawowa ba,hawaye suka kwaaranyo daga idanunta toni mena yiwa wannan yarinyar take qoqarin ganin bayana ,tunda nake da usman  bansan yanada wacca yakeso ba face ni kadai kuma bansan ina ya shiga ba ban taba yiwa wata snatchin ba ballantana `yar nan cikin kaduna garinda ban taba xuwaba sai yanxu,ta fashe da matsanancin kuka wai meke faruwa dani ne,rarrashinta ya ci gaba dayi,Bilkisu ki tuno inaso ki tunano koda abu kwaya daya da kika sani danganeda wannan yarinya.Ni bansan komai dangane da wannan yarin yar b aba abinda na sani ban santa ba,tana fada tana kuka,baba idan dai usman ne silar duk wannan abin to me yasa shi ba xatab hukuntashi ba me yasa shi ba xata dauki fansa a kanshi ba sai a kaina,Bilkisu ki sani wannan fatalwar xata iya cutarda kowa a duniya hatta ma iyayenda suka haifeta amma sam ba xata iya cutarda usman ba kuma ba xata taba yarda a cutarda shin a,ta kasance tana matuqar sonshi so mai dimbin yawa wanda shi yasa sam bataga laifinsa ba koda kuwa da daqiqa daya ga baki daya ta dora laifinne akanki kuma duka mummunan qudure-qudurenta a kanki ne ke kadai bada usman din ba. Ga baki daya ta rasa yanda xatayi duka kanta ya kwance ta rasa gane komai can ta samu ta bude baki tace baba na roqeka ka taimaka mani ta fadi akan gwuiwowinta tana roqonshi da hanxari ya tayadda ita Bilkisu taimakonki ya xama dole a gareni koda ba domin komai ba ko don dana kwaya  daya tilo da nakeda shi a duniya kuma ko a dalilin yadda kuka tausaya mani yadda kuka riqeni alhali bakusan koni wane ba ko kuwa domin sulaiman yaro mai hankali da tunani ga jinqan na qasa tabbas! Na aikata babban kuskure a baya ya xama dole a gareni na walwale wannan qullin koda kuwa shi xaiyi qarshen raayuwata la`alla na samu rabo a wurin ubangiji na miqewa yayi xumbur!Bilkisu bamuda lokacin bat lokaci kin shirya jure duk wata wahala da qalubale da xaki fuskanta domin ceto mijin ki daga hannunh wannan hatsabibiyar,itama tamkar a filin horarda sojoji miqewa  tayi sabon qarfin xuciyaa taji ya shigeta da qarfi ta bude baki tace a shirye nake na bada rayuwana domin ceto masoyina abin alfaharina daga hannun wannan axxalumar koda kuwa hakan yana nufin mutuwana ne baxan taba gajiya ko saurarawa ba koda kuwa sun kasance su dubu dari ne xan shirya damarar yaqi dasu kuma na tabbata ni keda nasara domin Allah yana bayan mai gaskiya,goge hawayenda ke kwarara tayi daga  idanuwanta kana ta fuskanci baba Tukur din baba me muke jira mu fara hanya domin ni a shirye nake kallonta yayi cikin jin dadi matuqa ya gyada kai kana yace nima a shirye nake sai dai tafiyar ba mu biyu kadai xamu yita ba akwai cikon mutum daya wannan kuwa ba kowa bace face Hajiya Larai! Yamutsa fuska tayi wanda yake nuna alamar wacece kuma haka,bai jira ta tambaya bay a shiga gaya mata kamar haka;bayamda naje dajinnan wajen binne magani da abinda ya faru dani idan baki manta ba bayanda naji furucinda fatalwar tayi shine na riqa xiyarar wannan gidan domin jiran xuwanku wata rana naje domin binciken ko kunxo,sai na samu yan sanda da mutane birjik a qofan gidannan bayanda na bincika sai aka gayamin wasu yara ne suke was an kwallo sai kwallon ta fada cikin gidannan,daya daga cikin yaran kuwa ya tsallaka ya fada cikin wannan gida domin ya dauko kwallon a yayinda su kuwa ragowar abokanan wasarsa suke jiransa a wajen gate din amma kwasam!sai yaran sukaji wata irin wargowa inda yaron ke kwarara ihu yana neman taimako su kuwa yaran dake jiran fitowarshi duka taewatsewa sukayi suka suka ari na kare  bayanda mutane suka kawo dauki koda aka shiga  ba yaro kwallon kuwa duka an yayyaga,a jikin bangon  kuwa aka rubuta “KADA WANDA YA SAKE SHIGOWA”da jinni kowa yayi tsammani da jinin yaron ne akayi rubutun amma bayan bincikenda aka gudanar sakamako ya nuna sam! Bama da jinin dam adam akayi rubutun ba,shi kuwa wannan yaron mahaifinshi ya kasance mai kudin gaske,su shida ne ga mahaifan nasu amma shi kadai ne namiji tun kafin kuwa a haifeshi mahaifinsa ya rasu,sunan mahaifinsa aka saka masa,mahaifiyarsa na matuqar qaunarsa fiyeda komai a duniya tun bayanda wannan abin ya faru wannan matar ta shiga rudani ita sam bata yarda a ranta danta ya mutu ba a kullum aganin takeyi danta yana a cikin gidannan  ya xama dole muyi wannan tafiyar da ita kamar wacca ta tuno wani abu ta xaxxare idanuwanta Hajiya Larai!Hajiya Larai take fada tabbas! Na tuna da wannan matar itace wadda ta taba far mani a gidan kitso tace na fitar mata da danta,shiru tayi kamar mai lissafi okay!na fahimta,sai yanxu na fahimta.Bilkisu lokaci yayi kije ki debi kayanki wayanda kike ganin xaki buqata a wannan tafiyar domin kuwa idan har muka fita daga gidannan ba xamu sake dawowa ba akwai abinda xan saka na kulle gidan dashi wannan abin shi xai taimaka mana wajen rufewa fatalwar idanu akan duk wani motsinmu xai sanya a duk sa`adda ta waigo gidannan ta riqa ganin kamar muna a ciki kinga tanan xamu samu mu danyi shir-shirye masu amfani ba tareda ta riqa bibiyarmu ba dukda yake shi wannan abin ba xai wani dade ba domin kuwa duk yadda kike tsammanin qarfin tsafin ta ya ninka haka a kowace daqiqa qarfinta qara qaruwa yakeyi dan haka sai ki shiryo mu tafi,da hanxari ta miqe ta nufaci daki ba tareda tace masa komai ba,kaya yan kadan ta diba kuma ta canxa wayanda take sanye,wata doguwar riga ta dauko baqa ta sanya kana  danyi jim tana duban abinda ke ciki kana tasa hannu ta fara dibar abinda ke cikin kudade ne masu yawan gaske xa`a iya cewa ga baki daya bankin sune,saida ta kusa kwashe duka kudin sa`annan ta raga yan saura ta janyo makulli ta kulle ta dura kudin a jakarda ta sanya kayanta a ciki ta kulle sa`annan ta fito,wurin meter taje ta kasha wutar gidan ga baki daya kana ta dauko jakar taxo daf da tsohon ta dubeshi tace na shirya,gyada kai yayi muje ko,suka nufi hanyar fitaa falon harta sanya qafarta xata fita falon ta juyo ta kalli falon hwaye masu xafi suka kwaranya daga idanuwanta kallon koina take tunanin masoyinta da irin rayuwarda sukayi a gidan kawai ke xiyartar kwakwalwarta da xuciyarta hotunansu ta duba da suke kafe a bango wasu sababbin wahaye suka sake xubo mata,dafata taji anyi ta juyo baba Tukur ne ke dubanta cikin  tsintsar tausayi baice komai ba gyada mata kai kawai yayi alamar kada ki damu komai xai dawo dai-dai,janyo qofar tayi ta kulle suka nufaci qofar fita daga gidan sake juyowa tayi ta kalli gidan har suka fice daga ciki,baba Tukur dinne ya sanya hannunsa a cikin qaton aljihun rigarsa ya fidda wani makulli saida ya karanta wasu dalasimai kana ya rufe gidan sa`annan ya fitarda wasu ruwa ya warwatsa a jikin gate din,gyada kanshi yayi alamar komai dai-dai ya juyo ya kalleta mu tafi ko.
    Tafiya sukeyi ba tareda an samu wani daga cikinsu yace uffan ba kowane tunani mai xurfi yakeyi basu yi wani nisaba Bilkisu kamar wadda ta tuna wani abu ta juyo ta kalleshi ,sai dai kuma bamusan gidan wannan…..bai jira ta kammala maganarda takeyi ba yayi caraf ya amsa nasan gidanta domin tunda abin ya faru nake bibiyar duk wani motsinta domin kawai xuwan irin wannan rana,gyada kai tayi kana ta budi baki da nufin amsa masa amma maganarsa daya sakeyi ita ta dakatarda tata maganar  nanne kusa ai ba nisa bayan wannan layinne ya fada,okay!kawai tace sa`annan su duka suka sa kai sukaci gaba da tafiya,basu jimaba suka iso a gaban wani katafaren gida.Baba Tukur ne ya fara tsayawa nanne gidan  ya fadawa Bilkisu  kamar wadda ta farka daga bacci ta fara ja da baya a’a inajin tsoron haduwata ta farko da wannan matar da kyar aka rabani da ita niyartayi ta kasheni ma,yanxu me kake ganin xata yimin idan har ta ganni har a cikin gidanta.ai komima xata iya aikata mani,Magana takeyi cikin tsiro da firgici kada ki damu da wannan Bilkisu xamuyi mata bayani fahimta,sa`annan Bilkisu keda kika shirya yaqi da wadda ta kasance bama mutum ba meye ba xaki iya jure abinda wannan Hajiyar xatayi,me xaisa kiji wannan da matsalarmu taxo daya mu duka,wadda kuma take mutum bil adama kamar ke,dadin dadawa ma abokiyar tafiyarmu kamar motarda aka sanyawa mai tace tabbas!maganganunka hakane ta wuce gaba da qarfi bakin gate din gidan suka tsaya a inda sukaci karo da mai gadi yana qoqarin rufe gate din gidan,juyowa yayi ya kallesu me kuke so bayin Allah,wa kuke nema, Bilkisu ce tace Hajiyar gidan muke nema. Hajiya Larai eyyah ai kuwa yanxu-yanxunnan ta fita yanxu-yanxunnan fah kunga ma ko gate din ban ida rufewa ba ma da qarfi Bilkisu tace a ina xataje ne,yaushe xata dawo,ai kuwa filin tashin jirgi ta nufa naji ance ko xata bar qasa ne…banda cikakken bayani dangane da tafiyar gaskiya.Ta ina ta bi,Bilkisu ta tambaya a firgice kinga ai kuwa gama motar a can ko qulewa basuyi ba mai gadin ya nuna mata da qarfin tab waiga ta kuwa hangi motar wurgi tayi da jakarda take daukeda ita ta xura a guje gudu takeyi ba qaqqautawa ihi takeyi tana kiran sunan Hajiyar.Mai gadin kallaonta yakeyi mamaki da al`ajabi ya cika shi ita kuwa gudu takeyi da duk iaya qarfinta gani takeyi kaamr ta rasa sulaiman dinta ne har abada idan har Hajiya ta tafi domin kuwa baba Tukur ya gaya mata wannan tafiyar sam ba xata yiyi ba saida Hajiyar .Qara takeyi mai tsananin gaske da sheqa gudu mai tsanani Hajiya! Hajiya! Hajiya! Take fada hawaye na kwaranya daga idanuwanta kaf! Ta jita a qasa sakamakon wani qaton dutse da qafarta ta buga rif!ta fadi a qasa wata irin mummunar faduwa tayi babban yatsanta kuwa wanda tayi tuntuben dashi jinni yakeyi ba qaqqautawa sam batamasan da jinmuwarda tayiba miqewa tayi yunquri tayi da qarfi amma taga motar ta tsaya cak! Baya-baya motar ta riqayi wanda yake nuna alamar Hajiyar ta jiyo ihun da Bilkisun keyi.Ajiyar numfashi Bilkisun tayi kana ta fasa dagowa daga faduwarda tayi daf a kusa da Bilkisun motar ta tsaya da qarfi aka bude murfin motar sai kuwa ga Hajiyar ta fito da saurinta,xumbur!Bilkisu ta miqe kallon-kallo sukewa juna kowa ya qurawa dan uwansa idanu sai kace wasu xakuna.Hajiyar ta fara bude baki tayi Magana me kike nema a gareni,ina dana,shi kika kawo mani,ta jero wayannan tambayoyin tana mai murtuqe fuska a’a bashi na kawo maki ba amma na kawo maki bayanai ne dangane da inda dan naki yake.Xare idanu tayi ta kafe Bilkisun da idanu a hankali-a hankali take tako ta nufato Bilkisun gadan-gadan caraf! Baba Tukur ya shiga tsakiyarsu  inda ya juyo da qarfi gami da bude hannuwansa alamar dakatawa ya fara yiwa Hajiyar bayani cikin dabara irin tasu ta tsofaffin bokaye masu ritaya.Danki yana cikinqoshin lafiya a wurinda danki yake kuwa a can mijin wannan yarinyar yake.Kallonsu takeyi su dukaa biyu ga baki daya fuskarta a yamutse a lokaci daya kuma fuskar tata ta fadada da farin ciki matuqa,dama na sani nasan khalifa yana a raye bai mutu ban a gaya musu amma sunqi yarda ina yake muje ku nunamin,hawaye suka kwaranyo daga idanunta dana khalifah kana ina kullum mummy sai kewarka takeyi,xaxxaro maganganu takeyi sai kace wacca ba tada hankali.Baba Tukur ne ya rarrasheta, Ya gayamata akwai buqatar su gana domin su samu damar fayyace mata daga biri har wutsiya.
    Ga baki daya a mota suka dunguma driver yayi reverse ya dawo baya hanyar gidan Hajiyar suka durfafa,sai a cikin farfajiyar gidan driven yayi parkingHajiya ta fara fitowa kana Bilkisu da Tukur suka fito.Iso tayi musu itace kan gaba biyun kuwa suna take  mata baya.A wni qaton falo suka iso wanda aka qawata iya qawatawa .A haqiqanin gaskiya komai kudinka idan ka shiga wannan falondole xakasan ya hadu iya haduwa,komai a falon kyalli yakeyi gwanin ban sha`awa ko electric bulb dinda yake ya falon kuwa abin kallone domin ita kanta Bilkisun sai a cikin film ta saba gani,ko a film din ma sai irin fina finan sarautarnan,wani irin qaton gilas ne mai matuqar kyawu,sai kuma windows inda suke a falon ga baki daya da tsintsar glass akayisu,abin gwanin ban sha`awa.Wuri ta nuna musu hadida yi musu umurni da su xauna,wani dogon frige ta bude ta dauko musu abinsha ta ajiye musu da  cups inda xasu tsiyaya abin shan a ciki,itama wuri ta samu ta xauna a dayan kujerarda ke fuskantarsu.Saida tayi ajiyar numfashi kana ta budi baki tace ina saurare,kowa ya dauka na samu tabin hankali ne tun bayanda dana ya bata amma Alhamdulillahi yanxu na samu wayanda suka fahinceni daman a sani khalifah bai mutu ba,kurba lemonda ke hannunsa yayi kana ya ajiye kofin ya kalleta suka fuskanci juna.Haqiqa danki yana a raye bai mutu ba inaso ki saurareni da kyau kiji a kwanakin baya da suka gabata…..ya shiga bata labara tun daga kanshi da abinda ya faru dashi har xuwa Bilkisu da yanda mijinta sulaiman ya salwanta da kuma shirinsu na xuwa ceto masoyan nasu komai rintsi komai tsanani.Bayanda ya kammala bata labarinne yaja dogon numfashi kana yace kinji abinda ya faru  da kuma abinda yake tafe damu.Hawayene suka xuba daga idanuwanta tsam! Ta miqe daga wurinda take xaune sai a wurin Bilkisu ta isa ta janyo hannuwan Bilkisun ta riqe ta fuskanceta tayi murmushin yaqe tace kiyi haquri Bilkisu na fahimci yanda kike ji domin kuwa duka raunin xuciyarmu daya ne.Akwai ranarda aka taba wayuwar gari ba mijina na shiga rudu da fargaba mara misaltuwa,a dai-dai lokacinda wasu sababbin hawaye suka sake xubo mata.Xamu nemosu a duk inda suke a duniya ,ko wacece wannan fatalwar xamu yaqetakuma xamuyi nasara kinji?itama Bilkisu hawayen takey gyada kai kawai tayi alamar eh batareda ta furta komai ba.Miqewa Hajiya larai tayi me muke jira,mu tashi mu kama hanya ga driver nan sai ya kaimu har inda xamuje.Murmushi Tukur yayi kana ya fara bayani kamar haka;idan da ace mota xata iya kaimu har inda xamuje  a sauqaqe Kaman yanda kike gani to kuwa bama xamuxo nan gidan domin muyi wannan tafiyar dake ba mu biyunnan kawai xamu iya biyan kudi a kaimu har wajen sai kawai mu dauko mijin Bilkisu da danki ganinshi kawai xakiyi mun kawo miki,ku sani inda xamuje ba wani mahaluqi a duniyarna daya isa yaje wurin ya kuwa dawo lafiya matuqar baya kasance hatsabibin matsafi ba,domin kuwa koda ba akan ita wannan fatalwar ba akwai tarin  dinbin miyagun halittu marasa imani da tausayi fantsame a cikin dajin,ko a cikin ifiritai da aljanu ma sai wanda ya amsa sunansa yake xama a dajin dukda kuwa a bincikenda yani na gano akwai wasu kadan daga cikin manyan aljanai musulmai a ciki.
    Shi wannan dajin ya kasance baqin dajine mai duhuwa gamida matuqar tsoro,ya kasance daji mai daukeda sautuna daban-daban wanda jinsu kadai ya isa ya haifarwa dan adam da bugun xuciya domin matuqar firgitarwa.Komai kuwa sihirinka baka isa ka shiga dajin ka fto acikin kwana hudu ba,ballantana a inda na binne maganin yanada matuqar nisa da hadari a duk cikin fadin dajin.Duk wata halitta da mutum xai gani a cikin wannan dajin kama daga dabbobin dawa harya xuwa tsuntsaye  sam! Ba dabbobin bane da gaske domin kuwa ba wata dabba data isa ta xauna  har tayi rayuwa a wannan dajin  koda kuwa da daqiqa uku ne ba tareda an kawar da ita daga doron qasa ba,nasan kuwa bakwa buqatar na gaya muku kwata-kwata ba service a ciki ballantana ace xa`a iya kiran wani,ya xama dole kuwa a garemu mu yada xango a duk sa`adda rana ta fadi domin kuwa komai haysabibancin dan adam  bai isa yayi kai kawo a cikin dajinnan  a yayinda rana ta fadi ba,sabili da miyagun halittunda  suke a ciki lokacinne lokacin  baje kolinsu muddin kuwa kayi ido biyu da abin a cikin wannan lokacin to sai dai wani bakai ba.
    Babban dalilinda ya sanya kikaji nace wannan tafiyar ba xata yuwuba saida ke Hajiya Larai shine ;ita wannan fatalwar da muke shirin fuskanta  ta kasance abu mafi qarfi da tsafi  a doron qasa a kowace daqiqa  qarfinta da tsafinta qara qaruwa yakeyi  ba kuwa komai yasa take samun wannan qarfin da qara bunqasa ba  face matsananciyar qiqayya da take yiwa mutane uku wato;Bilkisu,qawarta da kuma mijinta  data kashe.Wayannan mutane guda uku qiyayyarsu itace makamashi wanda a kullum yake qara rura wutar fansa a wurin wannan fatalwar mu kuwa matsancin soyayyarda muke yiwa mutane uku shine xai bamu damar karawa da ita,kunga kenan qiyayyar mutum uku idan aka hadata da soyayyar mutum uku  qarfi xai iya xuwa daya bi ma`ana munasa ran xamu iya gwafxawa da ita dukda yake ita ba mutum bace kamar mu.Dogon numfashi ya aje a yayinda yakai nan a xancen sa,matuqar anaso ayi nasara akan wannan fatalwa ya xama dole mu shiga tarihinta ma`ana  mu binciko koi ta wacece waye ita?ku sani ba xaka taba yin fada da mutum kayi nasara ba matuqar  bakasan koshi waye ba.Yanxu fatalwace ita ya xama dole agaremu  mu gano wacece MARYAMA meye asalinta meye labarinta  ita wacece daga ina kuma,sanin wayannan abubuwa su xasu taimaka mana a wajen cin nasara a kanta.A yayinda ya kawo nan a xancensa  kuwa sai yayi tsi! Kamar wanda ruwa yaci,ya riqa dubansu,suma duban nashi sukeyi ga baki daya hankalinsu yana a kanshi.Bilkisu ta samu tace to a ina xamu fara neman tarihin nata?ta fada tana mai wurga mashi wani kallo irin wanda yake nuna kaifa muke ji dinnan.Dogon numfashi ya saki kana ya fara da girgixa kai nima ban sani ba domin iya bincikenda nayi na kasa gano komai dangane da ita wannan fatalwar,Sai dai mutum daya ne yakeda amsar duk wata ambaya  da muke nema wanda shi kadai ne xai iya warware mana  abinda ya shige mana duhu wannan kuwa ba kowa bane face USMAN!


Xaxxare idanu Bilkisu tayi meye ruwan Usman da wannan abin? Mu kadai wannan abin ya shafa,caraf!Bilkisu ta fada.Usman kuwa yakeda ruwa a ciki domin kusan duk a kanshi ne muka tsinci kanmu a cikin wannan yanayin ,idan bashi ba bamusan wani wanda xai gaya mana  wani abu daya danganci wannan fatalwar ba,wannan wace irin Magana ce kakeyi haka?a ina xamuga usman?ta inama xamu fara nemansa,koni da muke gari daya dashi bansan gidansu bat un kuwa bayanda yaxo yayi bamkwana dani ya gayamin xaije bautan qasa ban sake ganinshi ba har bisa ga haxal yanxu ina kake tunani to xamu ganshi? ko shekara  nawa xamuyi muna nemansa ba xamu taba samunshi ba domin kuwa ko sunan mahaifinshi ban sani ba bare muce a shiga internet ayi sarching ko xa`a dace,gashi kuma banada hotonshi ko daya ballantana mu bubbuga mu riqa rabawa mutane ko xamu samu wanda ya sanshi ko ya taba ganinshi.ya kakeso muyi shiru tayi kana hawaye masu xafi saka xubo daga  idanuwanta  wannan wace irin masifa ce haka,shin menene yake faruwa dani  ne dirsham! Ta fadi akan lallausan kafet inda yake shinfede a falon ta fara rera kuka mai ban tausayi oh! Ni Bilkisu na shiga ukubanida kowa kuma bansan kowaba ,mijina ya bata bansan cikin halinda yake ciki ba yanxu haka,hannu tasa ta goge hawayenda suke wanke mata fuska;Usman! Usman! Usman! Ta fada da qarfi ka tarwatsa rayuwata haduwata da kai sam ba alkhairi bace kaine sanadiyar duk wani qunci dana shiga a rayuwa haqiqa haduwata da kai baqar qadara ce domin kuwa ta sanya har yanxu nake nadama.Hajiya Laraice ta durqusa a qasa ta kama hannuwan Bilkisu a karo na biyu ta riqa rarrashinta har saida ta dan tsakaita kukan da takeyi kana tace mata Bilkisu a halin yanxu kece mafita a garemu ya xamma dole ki gaya mana duk wata hanya da kika san xamu iya bi domin mu hadu da shi usman,ki sani shifa kadai ne makulli a garemu wanda xai bude mana qofar da xamu bi domin  cimma manufofinmu na alkhairi,me kika sani dangane da shi ki tuna Bilkisu ko meye ki tuna.Shiru Bilkisun tayi da xarar kuwa ka ganta kasan tunani takeyi,qoqari ne takeyi taga ko xata iya tuna wani abu wanda xai taimaka masu wajen neman usman din,sai da ta kusa kai mintuna uku kana ta daga kai ta kalli Hajiya Larai bansan komai dangane dashi ba,baxan iya tuna komai ba,haka ta ringa fada tana girgixa kai kana tana kuka mai ban tausayi,kayi haquri baba Tukur bansan ta inda xamu fara neman usman ba,bansan komai dangane dashiba,hawaye na xuba mata,kallonta yakeyi ga baki daya tausayinta ya kama shi,Hajiya Lara ice ta tayarda ita Bilkisun;kada ki damu bakiyi laifi bas am wai domin kawai bakisan inda xamuga usman din ba,kina cikin rudani da tashin hankali ne yanxu duk yanda kikayi qoqari ki tuna sam ba xaki iya tunawa ba akwai buqatar ki huta kid an samu natsuwa koda na kwana uku ne,karfa ku manta gaggawa aikin shaidan ne muda mukeso muyi nasara sam bai kamacemu da muyi gaggawa ba,muna buqatar mu shirya kanmu kama daga irin guxurinda ya kamata mu tanada harya xuwa irin tanade-tanaden da ya dace ace munyi kafin mu afkawa shi wannan hatsabibin dajin a kwai  buqatar kidan samu lokacin kanki kiyi tunaani wata qila a dace mu samu a binda muke fatan samu,juyawa tayi ta kalli Tukur wanda tuni yake gyda kai alamar yayi na`am da wannan xancen dari bisa dari  tabbas! Wannan ba tafiya ce da takeso ayita a cikin tsanake sam bata buqatar garaje domin kuwa tafiya ce da take qunshe da dumbin rudani da rikitarwa a ciki,dolene kuwa mu shirya tsaf!domin ganin mun cimma burin abinda muka fata.Dagowa Bilkisun tayi a`a sam! Baxan iya koda kwana day aba tareda naje neman mijina ba masoyina abin alfaharina ta yaya xan samu natsuwa bayanda dearest dina baya a tareda ni ta yaya xan samu na huta bayanda nakeda tabbacin duk inda mijina yake ba a cikin hutu bane,dan Allah kada ku yanke irin wannan danyen hukunci haka domin kuwa xuciyata ba xata jure ba,sake fashewa tayi da matsanancin kuka mai ban tausayi da karya xuciya,ga baki daya tausayinta ya rufe su,kallonta sukeyi cikin tausayawa da jin qai amma ba yadda xasuyi dolene su dakata koda kuwa na kwana biyu ne,domin suyi tunanin ta inda xasu fara neman usman kafinma aje batun waccan fatalwar,ba yanda suka iya dole ya xamar musun domin koda sun fita a yanxu basusan inda xsu dos aba.Da kyar! Suka samu suka rarrasheta ta amsa musu akan abinda suka ce,a kuwa gidan Hajiyar xasu xauna su duka kafin su kammala duk wani shirye-shirye da xasuyi ta yadda ita Hajiya Larai  bayanda ta kira driven ta,ta hadashi da Tukur domin ya kaishi masauki.Miqewarda Bilkisun tayi Hajiya Laran ta lura daa jininda ya rufe dan yatsan na Bilkisu,subhanallahi!Bilkisu kinji ciwo a qafa,da hanxari Bilkisun ta duba qafar tata lallai kuwa ba qaramin rauni taji a qafan tata ba,sai ma a lokacin ta lura da haka kana ta tuna da inda ta samu raunin.Tashi muje a clinic a wanke maki,a`a Hajiya idan da first aid box ma ni xan iya yiwa kaina komai,kin tabbata Bilkisu da dai kin bari kawai muje clinic din Hajiya larai ta fada cike da damuwa,kada ki damu Hajiya nixan iya yiwa kaina,okay! Hajiya ta fada kana taje ta dauko mata first aid box din,ta taimaka ta bude mata first aid box din,sa`annan kuma ta taimakawa Bilkisun tayi treating din ciwonda taji,sa`annan ta mayarda box din a inda ta dauko.Muje na nuna miki inda xaki xauna,ta janyo hannunta ,wani daki suka isa mai kyau dashi,Bilkisun ta xauna ita kywa streat a ban daki ta nufa ta kunna na`urada ke dumama ruwa kana ta fito da `yar fara`arta ta gayawa Bilkisun taje tayi wanka ko xata samu tadan huta,gyada kai kawai Bilkisun tayi tareda yin murmushin yaqe,kama hanyar fita dakin Hajiyar tayi har ta kai qofa kuma ta tsaya kamar waccca ta tuna wani abu sai kuma ta juyo tace yauwa idan kuma kinaso kiyi kallo idan kika fito daga wankan xaki iya kunnawa ga kayan kallon nan remote yana a cikin drower din can ta nuna mata da dan yatsa.gyada kai kawai tayi okay na gode Bilkisun ta fada itama Hajiyar gyada kai tayi duk abinda kuma kike buqata ki hau a sama ki sameni ki gayamin kin ji,eh kawai Bilkisun tace Hajiyar tasa kai ta fice.Saukarda kanta tayi a qasa idanuwanta suna kallon qasa amma a xahirin gaskiya ga baki daya tunaninta baya ma a dakin ,ba abinda take tunawa sai mijinta masoyinta abar qaunarta,me yasa fatalwar xata daukeshi,ita ya dace ta dauke domin itace wacca takewa qiyayya,meye laifin sulaiman a ciki,a wani gefen kuwa takaicin usman nen yake damunta,sai a lokacin take bawa kanta laifi,shin ni wai meya kaini yin soyayya dashi,maybe ma alhakin ummanta ne saboda rashin gayamata da tayi da irin soyayyarda ta yi a sirrance,maybe data gayawa ummanta da abin baxai taba juyewa ya xama hakan ba.Dogon numfashi ta saki kana ta fada toilet tayi wanka.Bata wani bata lokaci wajen shafa mai ba ta bude Jakarta ta dauko Hijab da Al`Qurani mai girma,daga kai tayi ta kuwa hango sallayer  a saman wadrof ,ta janyo ta shimfida ta fara karatun Al`qurani,sai da ta dade tana karatun har saida bacci ya shareta anan bisa priyer mat din ta shingida.Misalin qarfe biyu da mintuna ta farka tsaki ta saki da taga lokacin axahar ma yanaso ya gauta tsam! Ta miqe ta fada ban daki ta dauro alwala bayanda ta kammala sallah kuwa ta sake janyo Al`quani ta shiga karantawa har sai da akayi la`asar kana ta ajiye tayi sallar ta la`asar sai bayanda ta kammala sallar ta la`asar ne sa`annan ta lura da wasu kuloli a gefe,ba shakka a yayinda take bacci ne aka kawosu,sam-sam ta manta da wani abu wai shi abinci sai a lokacin ta tuna ga baki daya bata ci abinci batun safe.Tashi tayi taje ta bude kulolin wani kamshi ne ya doki hancinta `yar gidantace kuwa wato taliya,dafa dukanta akayi,taji vegetables harta gaji,koda kuwa bakajin yunwa kayi arba da abincinnan to tabbas sai ya shiga ranka domin kuwa an hadashi iya hadawa.Xaunawa tayi dirsham! A qasa  ta bfara cin abincin kai tsaye,batayi wani dadewa tanacin abincin ba sai kawai ta xame hannunta daga cikin kular a hankali,wani abune ya fado mata a rai,tayaya xata iya cin abinci irin wannan alhali kuwa mijinta wanda ta dalilinta ne duk wannan abin ya faru dashi yana can cikin wani hali wandan sai Allah ma xaiga abinci ballantana har yaci,hawayene suka kwaranyo daga idanunta ta miqe ta fada ban daki ta wanke hannunta ta rufe kulolin ta turesu a gefe.Saman prayer mat din ta sake hawa ta janyo tasbi ta riqa yiwa annabi salati tana neman mafita a wurin ubangiji,haka taci gaba dayi har bacci ya kwasheta a karo na biyu.Bubbugata taji anayi a hankali-a hankali ake kiran sunanta da qarfi ta bude ido  gamida xabura! Nice Bilkisu Hajiya Larai ta fada a yayinda taga kamar Bilkisun ta firgita,lokacin sallah yayi anyi kiran magarib sai ki tashi kiyi sallah kinji,gyada kai tayi ta saki fuska tau Hajiya ta miqe ta nufi ban daki domin tayi alwala ita kuwa Hajiya ta fice abinta,a sallar magarib bayanda ta kamamala sake dauko Qur`aninta tayi ta karanta bayan tayi nafil fili har aka kira isha sa`annan ta tashi tayi sallah kana ta durqufa da karatunta.Tabbas!Qur`ani waraka ne a wurin kowane musulmi domin kuwa komai quncinda ka samu kanka a ciki ka janyo Qur`ani ka karanta tabbas!xakaji sauqi a ranka kuma xaka samu nutsuwa.Bayanda ta kammala karatun nata  ta daga hannaye ta roqi Allah sarki gagara misali mabuwayi akan ya shige mata gabayayi mata mafita acikin halinda ta tsinci kanta a ciki,bayanda takai hannuwa da nufin ta shafa fuskarta  ne;raf! Raf! Taji ana tafa mata Wow! Masha Allah! Da hanxari ta waigo inda ta ga wata yarinya xaune akan gadonta kyakkyawa da ita ga  baki daya shekarunta ba xasu wuce sha bakwai xuwa sha takwas ba gaskiya you have a nice voice the way you recite wow masha Allah,yarinyarce ta fada tana mai nuna jinjina ga Bilkisu wanda yake nuna alamar ta jima a wrin Bilkisun dai ce bata ganta ba.A bangaren Bilkisu kuwa ga baki daya kanta ya kwance wannan wace yarinyace da har ta shigo dakinda take a ciki ba tareda ta ganta ba,xaxxare idanu kawai tayi tana kallon yarinyar ,meya faru naga Kaman kin tsorata da ganina,to da farko dai ni aljanar wannan gidan ce,kasancewata a gidannan shi yake sanyab kowa farin ciki da annashuwa,Dam! Bilkisun taji gabanta ya fadi shedarata kuwa tana batun kwace mata aljana kuma,bata samu daman cewa komai ba kawai tsareta tayi da ido,dariya rayinyar tayi  kana tace nice autar mata a gidannan nice sirrin farin cikin wannan gidan ummana ta gayamin duk inda nake nakan kawo farin ciki a wurin shi yasa babbar yayarmu take kirana da aljana.Sauke wani numfashin tsoro Bilkisun tayi domin kuwa sai da yarinyar tayi wannan bayani ne ta gane `yar qaramar diyar Hajiyar ce,murmushin yaqe tayi tareda sake fuska.Yarinyar ta gaya mata umman ta ce tace taxo ta kirata domin suci abinci.murmushi Bilkisun ta sakeyi a karo na biyu okay! Ta miqe ta nadiye prayer mat  dinda take a kai kana ta dauki Al`Qurani takai a saman drower da take a kusa da bed ta ajiye,ta juyo to mu tafi ko tareda kallon yarinyar ,miqewa yarinyar tayi to aunty,yaya sunanki Bilkisu ta tambaya a yayinda suka kama hanyar xuwa dining,sunana Bilkisu amma friends ina sukan kirani da Billy bilisco dukda dai ban cika son a kirani da sunannan ban a fi daso a kirani da princess,ko banyi kama da irin princess dinnan ba please,dariya Bilisu tayi  a lokaci daya kuma mamaki ya dabaibayeta kinga kuwa nima sunana Bilkisu kuma nima akwai wanda yake kirana Billy amma fa da dadewa sai dai ke kinyi kama da princess amma ni kuma banyi ba.A dai-dai lokacinda suka iso dining din,Bilkisu qarama ta fashe da dariya a`a wallahi aunty takwara kinfini ma kama da princess kinada kyau sosai kuma kinada qira`a mai dadi,dariya suka saka su duka harda Hajiya Larai da suka tarar a dining din tana jiransu.Princess kin fara ko karfa ki cikata da surutan nan naki domin it aba irinki bace pirot da bakinta baya gajiya da surutu,dariya suka sake su duka,ai ko mummy surutu abune mai kyau kinji fa ance ko shaik Kabiru Gombe cewa yayi yanada kyau mace ta iya maganganu domin a koda yaushe mijinta ya riqa daukin xama da ita,ajiye cokali Hajiyar tayi oh! Ni oh! Ni `ya su yau Allah ya kaini ya nuna min yarinya qanqanuwarda idan dai ta xauna batayi maganar aure ba ko dadi bataji,ta gyada kai,su duka dariya sukayi.Abinci sukeci suna `yar fira kana Bilkisu ta fara miqewa bayanda ta kammala cin abincin,sai da safe tayi musu sa`annan kai tsaye ta nufi dakinta.Fadawa kan gado tayi kai tsaye ,fuskarta na kallon rufin dakin,tunani ta hau yi kala-kal.Babban gurinta a yanxu shine  a ina xasu gan usman,ta ina take ganin xa`a nemoshi how,ta yaya,ya xama dole a gareta ta nemo wannan amsar.Wuf! taji an fado saman gado da qarfi ta xabura domin taga ko waye,aunty takwara tunanin me kikeyi haka,ta tambayi Bilkisun fuskarta cikeda fara`a,murmushi Bilkisu tayi ba komai ba,ina kwance ne kawai gyada kai kawai princess tayi alamar okay! Na gamsu kana ta xarce da Magana,aunty takwara wai ko kinsan ko shekaruna nawa,ta fada tana  mai xare idanu tana duban Bilkisu ,murmushi Bilkisu tayi ta girgixa kai a`a,yauwa! Ai ni nasan ba xaki gane shekaruna ba,kinga ni shekaruna goma sha bakwai ta fada cikin alfahari da taqama,shekaruna sha bakwai kuma yanxu haka ina a s.s2 ne kinga shekara daya ya ragemin na kammala secondry,a wannan karon dariya Bilkisu tayi  daga nan kuwa sai jami`a ko kuwa school of nursing kike so gaya mani,a`a ba ko daya aure dai,ME! Bilkisu ta tambaya  a lokaci daya kuma ta tuntsure da  dariya,okay! Da gaskiyar Hajiya kenan da tace idan dai bakiyin maganar aure ba sam! Bakya jin dadi,da gaske auren xakiyi,idan kika qare secondry.Allah ba wasa a ciki wallahi aure xanyi aunty takwara xa xarar na kammala karatuna,barin dariyar tayi okay! To wanene mijin,waye shi.Numfashi yarinyar ta sauke babu shi aunty takwara ta dan ja gajeren tsaki mts!,dariya Bilkisu ta bingire da ita me kika ce,ba mijin,eh! Amma nasan a duk inda yake xaixo ya sameni,Allah ya umurcemu da muyi aure duk kuwa wanda ya sanya abin a ransa ya kuma yi yaqini mai kyau danganeda haka to ba shakka Allah xai taimaka masa ya cika masa wannan buri nashi na alkairi,ba komai yasa nakeson aure a rayuwana ba sai domin kawai shine martabar ko wace `ya mace a duniya inaso ne nayi aure domin na samu wanda xai riqa tsayamin a koda yaushe ,wanda idan nayi kwalliya xai kalla yaji dadi a ransa,domin kuwa na qara samun lada,me yakai aure kwasar garabasar lada a duk fadin duniya abinda annabin rahama manxon tsira Muhammad(S.A.W)yace duk wanda yayi aure ya cika rabin addininsa kawai abinda yayi masa saura shine yaje ya nemo rabin.Dangane kuma da abinda ya shafi al`amarin xaman aure kusan ma nace ba wanda yakai matar aure garanteen shiga aljanna,domin kusan duk abinda tayi lada ne,kama daga wanka,sanwa,tsaftar gida kai hatta murmushinda xaki yiwa mijinki ma lada ne,to me xai hana ba xanso wannan garabasar ba,me yasa baxanso nima nayi aure ba domin na raya sunnar manxo babba aunty takwara wayannan sune dalilaina koda xan dace na kasance cikin wayanda xa`a bawa littafinsu da hannun dama a gobe qiyama.Tsit! Bilkisu tayi tana kallonta a haqiqanin gaskiya da farko na dauka princess irin yarannane da  sangarta tayiwa katutu a kai,amma sai a yanxu ne ta fahinci wacece princess;yarinya kyakyawa ta gaban kwatance ga ilimi ga kuma sanin yanda ake sarrafa harshe,lallai kuwa wannan yarinyar ta cancanci jinjina lokaci daya kuma tumanin masoyinta ya fado mata a rai,sauri tayi ta kawarda wannan tunanin sa`annan tayi murmushi yaqe,tabbas! Duk abinda kika fada gaskiya ne aure rahama ne yinsa kuwa samun nutsuwa ne .Princess bata jira Bilkisu ta kammala maganganunta ba yauwa! Aunty takwara mummy na ta gayamin matar aure ce ke,murmushi tayi ta gyada kai tace eh!ina mijinki yake ne aunty takwara.Dam! taji xuciyarta ta buga kamar wacca aka bugawa qaton dutse a xuciya,amma ta daure bayanan ya bata amma xan nemoshi duk inda ya shiga a duniya koda kuwa xan rasa tau rayuwar ce wajen ceto tasa,kallonta prinncesss keyi cikin tausayi;na fahimta aunty takwara nima qanina ya bata,amma karki damu in Allah ya yarda xaki nemo mijin naki kuma xaki sameshi cikin qoshin lafiya,murmushi Bilkisu tayi insha Allah.To a ina xaki fara neman nasa,kin kai hotonsa a gidan talabijim,da ofishin jami`an tsaro haka ma ina fatan kin saka hotonsa a kafafen sada xumunta,a`a banyi kom day aba,ba xaki fahimta ba princess kafin na fara neman nashi sai na fara neman wani daban wanda shi muke sa ran xai bamu bayaninda xai taimaka mana wajen nemo mijin nawa,okay! Shine wanda xai gaya miki inda mijin naki yake kenan ,da sauqi tunda har akwai wanda yasan inda yake,cije lebe Bilkisu tayi I wish!naso ace yanda kikace diinan hakane amma kuwa ba yanda kike tunani bane shi wannan da xamuje nema xai kawai samu a hanya ne Hmm! Dogon numfashi ta saki a yayinda ta kawo nan a xancenta,duk yanda nayi miki bayani ba xaki fahimta ba,kana tayi shiru na `yan daqiqu kadan sa`annan  ta dago ta kalli princess;ban san ta inda xan nemo wannan mutumin ba princess,bansan ta inda xan far aba,bansan komai dangane da gidansu ko inda xan same shi ba.Shiru princess din tayi tana dubanta itama,anan garin yake ne,princess ta tambaya,a`a ta girgixa kai sam! Ba`a garinnan yakeba,a garinmu daya dashi dan adamawa ne shi,amma bansan gidansu ba,unguwarsu fah,princess ta tambaya,har yanxu idanuwanta suna akan Bilkisun.Shiru Bilkisun tayi na “yan mintuna ga dukan alamu tunani takeyi;Unguwarsu! Unguwarsu!! Haka take fada a hankali-a hankali tana qoqarin browsing din amsar a kwakwalwarta,dagowa tayi da qarfi bata jira Bilkisun ta baydda amsa ba ta xarce da maganarda takeyi,da ace kinsan unguwarsu da abin xaixo da sauqi,domin kuwa idan kikayi la`akari da wayanda suke rarraba maganin poli`o,gida-gida suke shiga suna bayarwa a yan kwanaki kadan kuwa sai kiga har sun kammala a unguwar ba gidanda basu shiga ba,haka xalika masu karbar kudin wuta suma fa a gida-gida suke xuwa kuma a iya kwanaki qalilan sai kiga sun kammala ko ince sun kammala da wannan unguwar,idan kinsan unguwarsu haqiqa ni a ganina kawai kubi gida-gida wajen nemansa na tabbata xaku isa gidanda yake komai girman unguwarsu,shiru bilkisun tayi na “yan mintuna  ga dukan alamu kuwa tunani takeyi,unguwarsu! Unguwarsu! Unguwarsu! Haka take fada a hankali tana qoqarin browsing din amsar a kwakwalwarta dagowa tayi da qarfi;Government  house anan Government house yake,dariya ta farayi a hankali wallahi a unguwar Government house yake murmushi princess tayi kana ta dafa ta good one aunty takwara,kiyi naxarin abinda na fada miki,ta miqe tsaye ni inaso na wuce inaso nayi bacci da wuri gobe nikeda duty a school ko ba domin dutyn da nakeda shiba ma discplin master yayimin qorafi da warnin akan xuwanda nakeyi makaranta late a matsyina na head girl,kinsan yanxu an damqawa ss2 komai sabida ss3 student suna final exam ne wai as a head girl I must show good example to the others for them to follow,ta wani yamutsa fuska irin kin gane ai,murmushi Bilkisun keyi sai da safe Princess thank you so much for everythin.Princess ta fice ita kuwa ta tashi ta kashe wuta kana ta fada a kan gado,wani dadi takeji mara misaltuwa xuciyarta kuwa xarya takeyi ta gayawa Hajiya Larai da Tukur ta gano mafita ta gano ta inda xasu nemo usman din,tamkar wacca ta farka daga bacci take jin kanta,me yasa wai ma batayi wannan tunaninba  tun a can farko,haqiqa princess yarinya ce nmai hankali da fasaha duk wanda yayi sa`a  ya aureta tabbas! Yayi dace a rayuwa.A haka Bilkisun ta kwanta cikin farin ciki da jin dadi,dauki takeyi gari yaw aye domin su nufi hanyarsu ta adamawa,wajen neman usman,ji takeyi kamar a gobenne xata ga mijin nata.

       Sulaiman ne daukeda wani jinjiri kyakkyawa gwanin ban sha`awa  a kusa da wata rijiya mai matuqar xurfi,sai wasa yake yiwa yaron,Bilkisu ce ya hango ta nufo inda yake su duka murmushi suke yiwa juna hannunta daya a baya wuqa ce kuwa ta boye a dayan hannun nata ta nuface shi gada-gadan,da isarta inda yake tayi wuf!ta caka mashi wuqar baya yayi taga-taga kamar xai fada rijiyar kallonta yakeyi mamaki cike a fuskarshi,har a lokacin kuwa yaron na a hannunshi ,da kyar! Ya budi baki yayi Magana;why,why,Bilkisu why,bata jira ya qarasa maganarshiba ta tunkuda shi a cikin rijiyar  dashi da yaron duka suka afka a ciki.Firgigib ta farka subuhanallah!Hasbunallahi wa ni`imal wakin! Ga baki daya ta jiqe da xufa sharaf! Kamar wacca aka watsawa ruwa,shima kuwa Alhaji Jamilu da yake kwance a kusa da ita  farkawa yayi da qarfi a sakamakon addu`arda matar tasa keyi da qarfi,lafiya,lafiya,lafiya,meya faru ya tambaya sai da tayi ajiyar xuciya ta sauke numfashi sa`annan tace wallahi mafarki nayi mugun mafarki,sulaiman ana gani….caraf! ya katseta ba sai kin fad aba,ba`a fadin mummunan mafalki,kuma shedanne kawai,Allah ya gaya mana mugayen mafarkai daga shedanne,Alhaji mafarkinnan ya firgitani matuqa,gashi da rana nayita nemansu a waya bata shiga,ta shi kuwa duka data matarshi bamusan meke faruwa ba ko lafiya.Dan qaramin tsaki yai ai kinga irinta,kice da abin kika kwanta kena shine shi kuma shedan yaxo yasa nashi kwaban,suna can qalau in Allah ya yard aba abinda ya samesu,da safe idan Allah ya kaimu sai ki sake kiran nasu kinji,yanxu dai kiyi addu`a sai ki canxa hannu,ki kuwa kwantarda hankalinki kinji sarkin son diya,ya fada yana dan tsokanarta,dariya tayi kawai ta bi umurnin mijin ta,ta kwanta dukda yake bacci ya kyauracewa idanuwanta,jira kawai takeyi safiya ta waye ta kira dan nata ko hankalinta xai kwanta ta samu sukuni.

       A can bangaren su Bilkisu kuwa baccinta tayi harda minshari tunda asubahi fari ta farka,ta fara nafilfili da roqon agaji a wurin mai duka har aka tayarda sallah,tayi sallah ta fada salatin fiyyenhalitta har a ranta tanajin nasara da sa`a na tareda ita domin kuwa tanaji a jikinta in Allah ya yarda xasu samoshi a nan ta duqufa har bacci yaxo yayi awon gaba da ita.Misalin qarfe takwas dai-dai ta farka,da sauri ta nadiye prayer mat ta hada da Al`Qur`ani taje ta ajiye brush dinta ta dauko daga cikin Jakarta ta janyo towel ta fada bathroom,bayanda ta fito ta shirya tsaf!cikin qanqanin lokaci ta fice daga cikin dakin,Hajiya Larai da Tukur ta hango a xaune a kan dining suna karya kumallo kamar sunsan hakan takeson ganinsu a kammale da hanxarinta ta nufi inda suke gaidasu tayi da kwana suka amsa mata,kana Hajiya Laran ta gayyaceta akan taxo tayi kari itama.Sai da ta xauna kana ta fara dayi musu bayanin abinda suka tattauna ita da princess a daren jiya,tareda basu tabbacin wannan ita kadai ce mafita kwaya daya da xasuyi amfani da ita wajen neman usman din.Ga baki daya sunyi na`am dajin wannan xancen kuma sun jinjinawa princess matuqa  tareda mamakin ta yanda akayi su duka suka kasa xuwa da shigen irin wannan tunanin tun a karon farko.Tukur ne ya qara  da tofa albarkacin bakinsa tareda yiwa Bilkisun bayanin koda fa sun shiga a Adamawa sam! Ba xatayi yunqurin xuwa gidansu ba ko gidansu sulaiman,domin yin hakan xai tarwatsa duk wani shiri nasu hadi da ruguxa komai a inda yaci gaba da gaya mata  dolene tayi taka tsam-tsam ta kuma kiyaye kada ta yarda wani ko wata wayanda suka santa  su ganta domin gudun abinda xaije ya dawo gyada kai tayi na fahimta,to sai dai a ina xamu xauna a iya kwanakinda xamuyi a can adamawa,Bilkisu ta tambaya kai tsaye.Hajiya Larai ta tambayeta akan ita `yar wace anguwa ce a cikin jemetar,180 unit, Bilkisu ta amsa  mata,okay ni kuwa kinga inada friend wacca take a karewa sai nayi mata waya mu sauka a can,toh! Suka amsa su duka,sai ku tashi mu fara shiri ai ko,Hajiya Lara ice ta fadi haka a yayinda take qoqarin miqewa,duka ntashi sukayi a lokaci daya kowa ya nufi dakinshi,domin su kimtsa,ita kuwa Bilkisu dama a shirye take tana xuwa xaro wayrta tayi sai da tayi mintoci tana duban wayan daga bisani kuma ta kunna wayar,number mahaifiyarta ta fara dannawa,bata jira ta wani yi ringing sosai ba ta dauka suka gaisa irinta da da uwa ta tambayi mahaifin nata,babar tata ta gaya mata ai tana tareda shi ma a yanxu haka,miqa mishi wayar tayi shima suka gaisa matuqa,yayi mata huduba akan ta riqe mijinta hannu bibbiyu kuma tayi masa biyayya sa`annan ya miqa wayar ga mahaifiyarta,har sunyi sallama xata kasha sai kuma tayi sauri ta gaya mata an fah tura mijin nata a can wani qauye inda ba service kuma a tare xasu je,kuma ba xasu wani dadewa ba insha Allahu dan haka koda ta kira ko mahaifinta duk dai wanda ya kira bai sameta ba kada ya tayadda hankalinshi suna lafiya,toh! `yar albarka Allah ya kaiku lafiya ya dawo daku lafiya ya tsareku kinji,ina gaida shi sulaiman din ta katse wayar hawayenda ke maqale a idanuwan Bilkisu ne suka kwararo,sun kai kusan minti biyu suna xuba,sa`annan ta goge ta kamo number surukarta,ringing daya kawai wayar tayi ta dauka `yar halak kinqi Ambato,yanxunnan na kamo lambarki ina batun na danna sai ga kiran ki ya shigo kuna lafiya dai ko,jiya na yita kiran number ki data mijin naki duk a kashe,lafiya qalau ummah jiya dai ba wuta ne mu duka wayoyinmu ba chaji,kai! Wai dan Allah ku me yasa baku damu da waya bane sam! Ai koba komai ya dace ku riqa barin wayoyinku a kunne koda xa`a kira aji lafiyarku,wannan ba shine na farkonku ba haka yasha faruwa a lokuta da dama sai nayita kiran wayoyin naku amma a kasha,ayi haquri umma xamu gyara,to kuna lafiya ya wajen naku,ya shi mijn naki,ina fatar dai ku duka kuna lafiya,surukar tata ta jero mata wayannan tambayoyi,lafiya qalau ummah Alhamdulillahi,suka gaisa abinsu daga bisani ta gayamata abinda ta gayawa babarta,itama addu`a tayi mata sosai kana da fatar Allah ya dawo daku lafiya,sukayi sallama ta katse wayarta sauke wayar tayi kana ta goge hawayenda ke xubowa daga idanuwanta,photos ta shiga kai tsaye.Hotunoninsu itada sulaiman ta fara cin karo dasu inda sukayi su biyu da inda yayi shi kadai,murmushi tayi tareda hawaye a lokaci daya,I miss him! I really miss him ta fada  a fili,fita tayi anan ta fada jerin videos,kullum kuwa aikin sulaiman bai wuce ya riqa daukanta video ba bi ma`ana videoting dinta,hannunta a kan wani video ya sauka,sulaiman ne ke qoqarin yi mata kitso a cikin videon,sai da ya fara bayani shi sunanshi Romeo,yana qoqarine yayiwa Juliet dinshi kitso,sa`annan ya saita wayar yanda xata riqa daukansu ba tareda ya riqa wayan a hannunshi ba,dangwala mata kai yakeyi,ash! Ash! Kaina take fada,tayi qoqarin tashi shi kuwa janyota yakeyi yana ci gaba da jagalgwala mata kai,da kyar ta samu ta kucce ta ruga a guje ya kuwa take mata baya….Rufe idanuwanta tayi kamar a film,ta riqa tuna abinda ya faru a wannan ranar ganinshi takeyi a idanuwanta kamar wacca aka kunnawa T.V a guje ta fada kan gado kafin tayi wani yunquri tuni sulaiman dinne ya danne mata hannuwa ko wannensu nishin gajiya yakeyi daga gudunda sukayi,qoqari ta riqayi domin ta kwace kanta,amma sam! Yaqi bata dama,gashinta da yake warwatsene ya rufe idaniyarta daya a qoqarinda takeyi wajen kwatar kan nata,a hankali yake busa gashin ya kuwa yi nasara iskarda yake busawa ta janye gashin, su duka qurawa juna idanu sukayi.Bude idanu tayi gamida yin murmushi da takai nan a tunanin ta,salamu alaikum! Taji sallama a bakin qofar dakinda take a ciki juyowa tayi yayinda taga Hajiya ce a tsaye ,idan kin shirya ki samemu a falo,ta wuce abinta. Da hanxari Bilkisu ta miqe ta kashe wayarda ke hannunta,ta janyo Al`Qur`ani da sallayer duka ta tura a jakar ta ta rufe sa`annan ta nuo falon da sauri ta kuwa tarar dasu kowanne a tsaye a cikin shiri ,muje ko Hajiyar tace ta shige a gaba su kuwa suna take mata baya,koda suka fito drivern su kadai yake jira,da hanxari driver yaxo ya karbi jakar Hajiya ya durata a boot,ita ma Bilkisu ta sanya tata a boot,sai `yar jakar tukur shima.Suka shiga a mota,Tukur shine ya shiga gaba su kuwa suka shiga baya,airport xaka kaimu,Bilkisu ta juyo ta kalleta,murmushi tayi tace ba muda lokacin bin mota Bilkisu,gyada kai tayi Allah ya qara budi inji Bilkisu,murmushi kawai Hajiyar tayi ba tareda ta furta komai ba,driver yaja mota ya nufi hanyarda xata kaisu airport.
       A airport din drivern ya tsaya da hanxari ya bude  boot din motar ya dauko traveling bag din Hajiya su duka kuwa suka fito a motar kowa ya dauki nashi,driver yayi lock din motar kana ya dafe musu baya,tafiya sukeyi ba wanda ke cewa komai kowa tunani kala-kala yake yi.A bangaren Bilkisu kuwa tunani takeyi yau gashi xataje a Adamawa ko a Adamawar a jimeta alhali kuwa ba xata ga mahaifiyar ta ko mahaifinta ba,xata shiga cikin garinsu ne tamkar wata barauniya,wani bangaren kuma tunanin mijinta ya fado mata,anya xata iya rayuwa ba tareda mijinta ba,kwana daya kawi amma ji takeyi kamar kwana dubu ne,ji takeyi kamar a qayoyi take yawo tafiya kawai takeyi amma sam! Hankalinta baya jikinta,ga baki daya hankalinta baya akan hanya tunaninda take duka ya tafi da hankalinta,kaf!! Tayi kaura da mutum,kayanda suke a hannunsa duka suka waste a qasa  da sauri ta duqa ta fara harhada masa kayansa,ga baki daya ta tsorata hannunta har rawa yakeyi.what the hell ix wrong with you! Don’t you have eyes!bakida idanune! Mutuminne ke mata tsawa cikin takaici,I`m sorry ta fada tana harahada masa kayanshi muryarta har rawa takeyi tsaki kawai yayi,wayarshi ta hanga a can gefe,sauri tayi ta kai hannu xata dauka alla-alla takeyi kada taga wayar a fashe domin kuwa idan har wayar wannan dan bala`in ta fashe  batasan iya masifa  da cin xarafin da xaiyi mat aba,dauko wayar tayi wayar kuwa na a kunne da hanxari ta duba screen din wayar,sake kayanda ta ta harhadawa mutumin  tayi suka sake faduwa a qasa a karo na biyu,hannu biyu  tasa  ta damqi wayar  ta fara miqewa a hankali,what do poke! Are you mad!mutumin  ya daka mata  tsawa a yayinda  yagata  sake barar masa  da kaya.sam ko  ajikinta bata damu da masifarda yakeyi.Abinda ta gani kuwa ajikin wayar  shine ya  jagula mata lissafi.Hotonta ne akan screen din wayar sa`adda shekarunta ba xasu wuce 16 to 17 years ba,kamar wacca aka xarewa laka a jiki ta fara juyowa a hankali browsing din muryarda keyi mata bala`in takeyi a kwakwalwarta ,wa xata gani a gaban nata,USMAN!




Danna wannan maballin (Click here to Read More!) don samun cigaban wannan littafi 

https://myscvonline.blogspot.com/2019/03/hubbul-yaqeen-payment-method.html

Za ku iya sada zumunci da Asiya Sadiq Maccido ta wanan layin 07088407665