SiraÉ—in So
Da Lafazin Soyayyah 2







SHARAHBIL MUHAMMAD SANI
(Sharhamak)
Tel: 08103139272
Copyright © 2015-11-02 Sharahbil Muhammad Sani MaÆ™era
Hakkin Mallaka © 2015-11-02 Sharahbil Muhammad Sani MaÆ™era

DOKA
An yarda ayi amfani da wannan littafi ko wani sashe daga cikinsa amma tare da kafa hujja dashi, tako wace hanya.


PUBLISHED IN NIGERIA BY
SIGNTECH DIGITAL PRESS LIMITED
No: 66/67 Beside Nagari Science College Birnin Kebbi,
Kebbi State, Nigeria

BOOK SETTING/COVER DESIGN BY
SHARAHBIL MUHAMMAD SANI MAKERA
Tel/WhatsApp: 08103139272






GODIYA
Dukkan yabo da godiya sun tabbatarma Allah Madaukaki, mai kowa mai komai, wanda Ya sanya soyayya a tsakanin jinsi biyu na halittarSa. Allah Ka yi dadin tsira ga Shugaban Halitta, Shugaban Annabawa da Manzanni, Muhammad Dan Abdallah (S.A.W) tsira da aminci su kara tabbata a gareshi tare da Iyalan gidansa da Sahabbansa da kuma masu bin tafarkinsa har izuwa ranar karshe.

SADAUKARWA
Ga masoya na nakusa da na nesa. Ina rokon Allah da Ya kareku daga sharrin makiya Ya kuma kara kulla soyayya tare da nasara mai dorewa, amin.

JINJINA
Gare ku masoya na makaranta littafai na da fatar zaku kasance a tare dani a koda yaushe.
Ina jinjina muku da irin kokarin da kuke da goyon bayan da nake samu daga gareku ta hanyar kira da aiko sako na fatan alkhairi da nake samu daga gareku, na gode. Na ku har kullum Sharahbil Muhammad Sani Makera (Sharha Mak)








SiraÉ—in So
NA AMINTA DA SOYAYYA
Na aminta da soyayya
Kaunar ki ce nayo niyya
Ke ce wacce nasa zuciya ta

Kaunarki ta zamto sarkakkiya
Rayuwa ta sa tayo farfadiya
Na rasa inda ni zan tsaya da kaunar ta

Rayuwa tamkar darbejiya
Da daci take tafi madacciya
Ya ki zo kice dani kin aminta

Zo kar kice dani kin kiya
In kinyi haka zan sakaya
Hankali zai gushe kanki masoyiya ta

A kaunar ki ni nake yin zabarbiya
Sauri nake yi bani gajjiya
Saboda son gimbiyar mata

Na aminta da soyayya
Kaunarki ni yau nai niyya
Ya ki yan mata

Na shiga rauni da zuciya
Amma na kasa tirjiya
Kaunarki ce ta sa ni gajjiya zo kice kin aminta

Sahiba ta zo ki bani soyayya
Aminiya ta kan ki bani alkunya
Sarauniya zo kice na aminta
SIRRIN ZUCIYA

Yau zan bayyana sirrin zuciya
Kaunarki ta sani hajijiya
Yaki kiban so kinjiya
Ke zaki barni na tsallake tsiradin zuciya

Gani gaban ki ina juyayi
Kaunarki ta sa ni nake juyayi
Lallai yau zan bayyana sirrin nadai na  boyoyi
yau gani na zo da sirrin zuciya

me sayasa a so na kasa yin tayi
kullum idan na ganki sai nai ta juyayi
kaunarki ta sa ni cikin juyayi
yaki amince da ni masoyiya

kullum idan na zo gidan ku sai na kasa tayi
kallun idon ki dai nai tsayi
kyakkyawar fuskarki ta sa ni tsayi
ina son ki yan mata amince da soyayya

kullum idaniya ta ke suke gani
sun makanta a mata basu gani
nayi nisa a soyayarki kizo ki gani
amince da ni kar kice baki so na masoyiya

kunnuwa na sun kurumta
basajin kira bale a furta
idanuwa ko sun azabata
da soyayyarki wata basu gani sai ke aminiya

kauna na bani kizo ki karba
yafi a ce dake kizo sharba
soyayyarki ce tasa ni nai ta kirba
bani son ace dani zan rasaki a soyayya

sirrin zuciya a yau na shaida
a zuciya ta babu tsida
gun wasu matan tayi tsada
ke kadaice zaki taya aminiya




















SIRADIN KAUNA

Siradin kaunarki zan tsallaka
Masoyiya ta zo ki taimaka
Ke kadai ce zan kusanta

Ina tunani a zuciya ta
Kaunarki lallai ta samu gata
Ke kadaice kauna na furta

Zo ki yarda dani aminiya
Kauna muyu da ke zo sarauniya
Tunani na bani da tamka ni na furta

Sanadin kaunarki na zama jarumi kauye da birni
A sonki na yi suna duniya anka sanni
Na samu masoya masu fata da alkhairi ni na furta

Amma gani yau siradin na kasa tsallakawa
Sai na fada don gazawa
Shin laifi na ne ko kuwa al’adar so tambaya ta

Nayi bincike kanki kuma na gane
Cewa ke ce wacce ta dace kuma na gane
Koda najje nai magana iyaye miji sunka mata

Nayi kuka idaniya sun gajarta
Zuciya ta sai faman bugawa kamar ta busta
Na kasa hakuri amma can sai sunka furta


Sun bani kauwar ta don ita an rigani
Nace zanyi shawara zaku jini
Da naje gida na bacci yaki zowa gareni, aminiya so zoki furta

Idan ka duba hannu na sunanta shine
Kullun itace abin tunawa, tunaninta shine
Abinyi gareni don na yi nisa a so ne zo na baki gata

Ina neman shawarar yan dandalina
Me zance gun mahaifanta don na nuna
Karfin soyayya ta gareta ko zasu gane zan bata gata

Wannan shawara ce ni na nema naji ta babba
Gunku masoya ni bani zamba
Ina sonta amma basu banba, aminiya zo na baki zuciya ta

Siradin kaunarki zan tsallaka
Masoyiya ta zo ki taimaka
Ke kadai ce zan kusanta

Ina tunani a zuciya ta
Kaunarki lallai ta samu gata
Ke kadaice kauna na furta








…BURINA

Bani sake soyayya
Bani sakara lobayya
Yau na juya baya

Na rasa farin ciki na
Mai haskaka ruhina
Mai tausayi ga kalbi na

Na zasa mai so na
Mun dade da son juna
Gashi yau iyaye sun raba mu da juna

Ni fa kece burina
Ke naso ace zan nuna
Surruka ga ummana

Meyasa kuke jifa na
Kuka nake kan kauna
Na rasa zabin kalbina

Masoyayi kizo zo guna
Zo kice kina burina
Aure muyoshi da juna

Zan rike amanar kauna
Zan tsare hakken mai sona
Ke ce muradin raina


Kaunarki ce burina
Kaunarki ta ratsan raina
In babu ke an barna

Farin ciki babu araina
Ya ke abin alfahari na
Zo nan kizo muyi kauna
























…MANUFATA

Sadiyya ke nake ta fata
Rayuwa ta duniya ke ce manuffata
Ina ta son su gane suna ta tsarguwa ta
Yaki zo mu zauna ki zam garkuwa gareni

Me yasa suka ce bazasu bani
Kudi, ilimi, nasaba duk suna gareni
Rikon da addini kuma dole gareni
Cikin masu hikkima dole ne a aganni

Na fahimta
Na aminta
Na karimta
Duniya ta sanni

Zainab ki ce ni
Zo muje ki bini
Muyi aure a birni
Na zo ki ganni










OYOYO MASOYIYA TA

Oyoyo masoyiya ta
Oyoyo zan baki gata
Oyoyo kaunar ki jata

Kaunar ki ta zama tsarin zuciya ta
Ke ce wacce na baiwa raggamata
Zo gani ki bani gata

Oyoyo sai na yaba ta
Kaunarki ce abin fadata
Sa’ida kin basu rata

Yau gani ina ta fata
Na so ace kudduri da fata
Sun cika yau na bata gata

Me yasa so yake da sata
Nan take zuciya ya sata
Yabi jini da jijiya ta

Gaki fara kuma kina da tsafta
Doguwa ce ga ido an bata
Tafiyar ta tafi ta, ai ta tsere mata

Ina sonki ya masoyiya ta
Kaunarki tana a zuciya ta
Zo gani ki bani gata

Sa’ida ce masoyiya ta
Kaunarki ina fadarta
A zuci kuma baki ya furta

Na aminta da son tauraruwa ta
Mai tsari irin na mata
Kizo gani ki bani gata






Soyayya! Soyayyah! Soyayyah!

Har yanzo ban dainaba
Kaunar ki ban fasa ba
Ni ke nasanya a rai duba
Ko zaki ce kina so na

Eh! Nayi tunani na duba
Kaunarki ta samin haiba
Kwarjini a cikin hubba
Har wayau ni ban daina ba

Har yanzo ban daina ba
Wayyo raina kaunarki ban daina ba
Tunanin ki shine abin yi duba
Hatsari na shiga kan soyayyar yar baba

Zuciya sai faman bugawa take zo duba
Na rasa sukuni kan sonki  akwana ban runtsaba
Safiya da rana duk daya ne guna basa gaba
Me yasa suke tunanin da ba’a karba












Sirrin Zuciya

Ke na baiwa sirrin zuciya
Kaunarki ta sani hajijiya

Tunaninki abinyi aminiya
Zo yaki yan mata zo Sa’ida

Kaunarki nai fata muje saudiya
Aure da ke nai fata masoyiya


Dare da rana kece tunanin zuciya
Har abada kece a zuciya

Idaniya na kuka kan masoyiya
Rabuwa ni da ke ban fata sarauniya

Ni bani zaton wai zamu rabu da taurariya
Tunani na ke nai duba a zuciya

Kina da kyan siffa ko ba kwalliya
Gaki fara, a sura sililiya

Iya tafiya kuma waye ba indiya
Tattausan lafazi








FIYA – FIYA
Sako daga Dan Kebbi
  
Agaida fiya fiya ka gama arna          -       kurungus angama da arna
Wa ye taure ya fada giwa                  -       kurungus angama da arna
Sun razana naga basu ima                 -       kurungus angama da arna
Kai har sun hankura sunga basu suna        kurungus angama da arna
Watturo taure ya fada giwa               -       kurungus angama da arna
Kanata hawa kana da girma              -       kurungus angama da arna
Kai ka kara hawa kana da girma       -       kurungus angama da arna
Sai dai gangara gwani na                  -       kurungus angama da arna
Kai dai sai dai gangara ubana           -       kurungus angama da arna
Gwarzo na Sa’ida basu cimma          -       kurungus angama da arna
Sharha Muhammad a gaida giwa      -       kurungus angama da arna
Dan bubawanga bashi ima                        -       kurungus angama da arna
kurungus mungama da arna              -       kurungus angama da arna
Sharha Muhammad kana da girma    -       kurungus angama da arna
Kai ga dan kasuwa tsayayye             -       kurungus angama da arna
Rana ta karo a baiwa giwa                        -       kurungus angama da arna
Wa yaro ya farma giwa                    -       kurungus angama da arna
Yanzu karonga basu ima                   -       kurungus angama da arna
Sharha Muhammad Allah daukaka ka       kurungus angama da arna

Sai dai Sharha na Makera ka gama da arna   kurungus angama da arna

Sannu fiya fiya ka gama da arna
Gaba dai Sharha Muhammad dan kasuwa ka darasu suna
Tafi dai tafi dai giwa haryanzu da kai mukai gwani na




Sannu fiya fiya ka gama da arna
Gaba dai Sharha Muhammad dan kasuwa ka darasu suna
Gaba  dai gaba dai giwa haryanzu da kai mukai gwani na

Bisimilla gwani ahadun sarki na mai dare da rana             -       Eh lallai
Shi yanda yaso yakai Allah na kar ka sani kuna                 -       Eh lallai
DK mai waka a jahar Kebbi zan buga tambari na              -       Eh lallai
A wajen gwarzon namiji Sharha Muhammad ubangidana

Sannu fiya fiya ka gama da arna
Muje Sharha Muhammad dan kasuwa ka darasu suna
Gaba  dai gaba dai giwa haryanzu da kai mukai gwani na

Salati dubu jimla zanyo gun annabi manzo na                   -       Eh lallai
Manzon Allah kunsan ya daukaka girma da suna               -       Eh lallai
Alihi da sahabai munsa suma sun daukaka da suna            -       Eh lallai
Ni dai manzon Allah kai dai ka kwanta zuciya na

Sannu fiya fiya ka gama da arna
Muje Sharha Muhammad dan kasuwa ka darasu suna
Gaba  dai gaba dai giwa haryanzu da kai mukai gwani na

Muna maganar Sharha Muhammad munsan kana da girma        -       Eh lallai
Kai ke bida maza Sharha Muh’d kanen Saratu uwa ta girma      -       Eh lallai
Karya yaro yashsha ya dangana don yaga bashi ima                  -       Eh lallai
Dan kasuwa mai kima ka zama fiya fiya na arna







Sannu fiya fiya ka gama da arna
Muje Sharha Muhammad dan kasuwa ka darasu suna
Gaba  dai gaba dai giwa haryanzu da kai mukai gwani na

Abin mamaki ga dan taure na fada da kura                -       Eh lallai
Yaja damara ya nade hannu ku kyale saura               -       Eh lallai
Kare a cikin jeji ku kunsan bai fada da kura              -       Eh lallai
Ga Sharhabilu Muhammadu ya kira su sauna

Sannu fiya fiya ka gama da arna
Muje Sharha Muhammad dan kasuwa ka darasu suna
Gaba  dai gaba dai giwa haryanzu da kai mukai gwani na

Gaba gwarzo mai Allah magauta ka sakasu kuka gwani na        -       Eh lallai
To yaya zasuyi ne ka gagara ka hanasu suna                             -       Eh lallai
Jirgi uban tafiya gwarzo na Sa’ida bashi sanya gwani na           -       Eh lallai
Sharha Muhammad ka daukaka ba’aja da maigidana

Sannu fiya fiya ka gama da arna
Muje Sharha Muhammad dan kasuwa ka darasu suna
Gaba  dai gaba dai giwa haryanzu da kai mukai gwani na

Ango ga Sa’ida gwani giwa kake masu kalle taru              -       Eh lallai
Gona mai taki can naffi zuwa na dinga lura                       -       Eh lallai
Ganda duk yayi noma fatan da yakai ga kwara                  -       Eh lallai
Har ya kai ga girbi gonar wani bata gaba nai







Sannu fiya fiya ka gama da arna
Muje Sharha Muhammad dan kasuwa ka darasu suna
Gaba  dai gaba dai giwa haryanzu da kai mukai gwani na

Gaba dai sharha jan zaki ka hana suna                               -       Eh lallai
Dotse mai nauyi kowaddauka shina da fama                     -       Eh lallai
Ya maliya tayi ruwa kai kogi saika ja da baya                   -       Eh lallai
Na Sa’ida ruwan malka kai muke so muke ta kauna

Sannu fiya fiya ka gama da arna
Muje Sharha Muhammad dan kasuwa ka darasu suna
Gaba  dai gaba dai giwa haryanzu da kai mukai gwani na

Kwaro yaja baya ya hangi fiya fiya makashi nai        -       Eh lallai
Shi ke karya maza ciwon ciki ka gama da irna          -       Eh lallai
Masaki ke karya kada kasu surazana ubana               -       Eh lallai
Kai nakawa waka banwa wawan da baida suna

Mai ilimin boko ga arbiya ina gwani na girma          -       Eh lallai
Ka fisu ado ka girmama naga basu cimma                 -       Eh lallai
Kafisu gida ka girmama naga basu ima                     -       Eh lallai
Dan kasuwa sharha kai munkafi so kai muka kauna




KARSHEN ZANCE!!!
Ashe waiwaye adon tafiya ne
yau ga masoyiya yar mama
Sa’ida ce yar mama nake nunawa
Yaki yar fara agaidake yar manya
Sa’ida ce yar Muhammad Usmanu karshen zance

Gaisuwa uwar tawaga sahiba ta ke zan yaba a yau yar girma
Na gaisheki sahiba takunki lafiya dai-dai-dai gaisuwa nake yi ta miki yar girma

Bisimilla sarki Allah wanda ya zamo gatana
Rabbana ka kara tsareni ya ubangiji sarki na
Zani na wurin Sa’ida gimbiyar yan mata, takon ki lafiya kin zam sarauniya yar girma

Ga salati gun manzon Allah don fa shi yazam gatana

Alihi, asahabatu na sanya kwarrike su bai koka ba
Tabi’ai waliya na sanya na rikesu ba sanya ba

Yanzu sharha zan dau hanya inje in iske giwar mata

Sha tankade da sabon kwarya!!!
Tasha ruwa da sabon muda..
Sa’ida ta zamo sai gada…
Maki gani ya runtse idanu na furta jinjina ga yar girma

Gimbiya Sa’ida, sannunki Sa’ida giwar mata
Ke alafiya kin tashi kwananki lafiya giwata
Sa’ida sannu hasken mata hasken ki ya wuce infurta
Gani naki Sa’ida tattaka a lafiya yar girma

Dukkaninku sai kunkai a kasa in kunga Sa’ida ta
Sa’ida yar gidan alfarma sannu sarauniyar mata
Akyau kin cire ta tutar nan ko wa biki sai yai rata
Gani sharha daga makera nazo wurin ki, kimin gata

Ke gadi girma kuma kin saba a gidanku ba karya ba
Ke gadi girma yar girma tun gidanku ba sanya ba
Maliya yau ta bamu ruwa tulu aja jiki can baya
In ana bayanin Sa’ida mata kuje kasa kuyi ban girma

Mata suka ce ga sako na jinjinar ban girma
Matan Kebbi sunke ga tasu jinjinar alfarma
Sakwkwato ma sunka ce in gaida sahiba yar girma
Yan yobe sun fada sun gaida yar gidan alfarma

Matan Abuja ma sunke sun gaida sarauniya yar girma
Matan adamawa suna kasa sunce a gaida ke maigirma
Matan Damaturu ma sunce ingaida yar gidan girma
Matan Sa’ida ma sunce sun gaida habibiyar alfarma

Sharahbilu jan karfe sararka anyi wasar banza
Kainuwa dashen Allah ne mai kinsa yayi shirmen banza

Sannu sannu manyan haraka taka a lafiya dan girma
Yau muna yabon Sa’ida dole ne muzo muyu ban girma

Ke fa sharha ya shedeki kin kara daukaka yar girma
Tunda sharha ya shedeki kin dinga daukaka yar girma
Ruwanki sun cika kofi kingi a barsu bakin kofa
Ta sharha kin gawurta wa zayaja da ke yar girma

Zo ki bashi kyautar zuciya don shi muke jira yar gata
Ni dan Muhammadu na roka zo aminta yar alfarma

Mugaida Zainaba yaya ga Sa’ida yar girma
Ita sarauniya Sa’ida naso na ganki inyi bangirma
Mata ga sharha kece fa shimfidar yan mata
Duk wanda ya ce zaija dake nasheda ba zaisha ba

Ke Sa’ida na gaisheki tunda kin gaida gimbiyar yan mata
Ke Sa’ida ikon Allah wa zayaja dake cikin mata?
Ke wucesu sun lamunta sun jinjina ga reki a girma
Kai a karonga sai na leka inganki sahibar yan mata

A gaida Aisha yar Sokoto na so na gaidake kin hidima
Hajiya Aisha Kano na gaisheki jinjina nake kin sha fama
Amina Yola ke ce jagora dole a gaidake yar girma
Zainab Kaduna a gaisheki ke ma nayo jinjinar girma

Lubabatu Kano na gaisheki kema kinyi kokari yar girma
Ina kike Zainab dole naje kano ban girma
Ina Sa’idar Abuja kinsha fama
Har wayau ina gaisheki Safiya a Abuja kinsha girma

Hakama balki na gaisheki yau har Kaduna zan ban girma
Saratu ma na gaisheki don kinyi hiddima yar girma
Habiba ma na gaisheki don kinyi kokarin bangirma

Go slow a sako a huta na dinga jinjina yan mata
Na gaidake yar girma don na sanki ba sanin banza ba
Amira kin sha hidima dole in hada da sandar girma
Hindatu Turaki a gaisheki dole ingaida ke yar girma 
 
Gaisuwa uwar tawaga sahiba ta ke zan yaba a yau yar girma
Na gaisheki sahiba takunki lafiya dai-dai-dai gaisuwa nake yi ta miki yar girma
Rubutawa Dan Muhammad
Birnin Kebbi 




KO KA/Ki NA JiNDADIN AYUKAN DA MUKE GUDANARWA?

Ga duk mai Sha’awar aiko da wani sako/abu da yake bukatar a saka masa a wannan shafi a matsayin nashi gudunmawa kai tsayi sai ya aiko mana sako ta wannan adireshin i-mel sharha089@gmail.com ko ya aiko sakonsa ta wannan lamba 08103139272, 0811377717.